• Leadership Hausa
Friday, December 8, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsofaffin mataimaka na musamman ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wadanda suka tsaya takara a jam’iyyar APC na neman kujerar gwamna da majalisar dattawa da na majalisar wakilai a Jihar Kano dukkan su sun sha kaye a zaben fitar da gwani.

Sun dai hada da Sha’aban Sharada, wanda shi ne tsohon mataimaki na musam-man ga shugaban kasa kan watsa labarai, wanda a halin yanzu haka shi ne shuga-ban kwamitin majalisar wakilai kan fasahar tsaron kasa da tsohon mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani, Bashir Ahmad da kuma tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan bunkasa zamantakewa, Ismaeel Ahmed duk sun sha kaye a zaben fitar da gwani da ya gabata a Jihar Kano.

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Ba Da Kyauta Ga Daliban Ghana Da Ke Fama Da Talauci

Sun dai sha kayen ne a hannun ‘yan takarar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mara wa baya.

Shi dai Sha’aban ya tsaya takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar, yayin da Bashir ya nemi samun tikitin takarar dan majalisa na mazanar Albasu/Gaya/Ajingi, sai kuma Ismaeel da ya nemi tikitin takarar dan majalisar dattawa na Kano ta tsakiya.

Ismaeel ya bayyana janyewar takararsa mintina kadan kafin gudanar da zaben fitar da gwani. Amma shi Sha’aban da kuma Bashir an gudanar da zaben fitar da gwanin da su wadanda suka sha kaye.
Bayanai dai sun nuna cewa, Ismaeel ya janye takararsa ne bayan da gwamna ya tabbatar masa da cewa Abdulsalam Abdulkarim Zaura zai bai wa tikitin takara.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Nijeriya Ba Sa Amanna Da Jam’iyyun Siyasa – Akpabio

Jega Ga Tinubu: Ka Sake Duba Nadin Kwamishinonin Zabe

Sha’aban dai ya samu kuri’u 30, yayin da abokin karawarsa mataimakin gwamna, Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya lashe zaben ya samu kuri’u 2,289.

Bashir dai ya samu kuri’a 16, yayin da abokin karawarsa da ya lashe zaben, Abdul-lahi Mahmoud Gaya ya samu kuri’u 109.

Masu sharhi kan zaben Kano sun bayyana cewa sakamakon zaben fitar da gwani na takarar gwamnan bai zo da mamaki ba, saboda Sha’aban yana takun-saka da gwamna da kuma shugabannin jam’iyyar APC na jihar tun a shekarar 2021.

Shi kuma Bashir a tunaninsa zai iya samun tikitin takarar dan majalisar wakilai ci-kin ruwan sanyi tun da dai ya kasance yaro ne ga fadar shugaban kasa kamar dai abokinsa Sha’aban, amma bai yi nasara ba.

Majiyar ta tabbatar da cewa, lokacin da Bashir ya bayyana wa shugaban kasa a niyarsa ta tsayawa takara ya amince da bukatarsa kamar dai sauran ‘yan takara da suka bayyana masa aniyarsu. Amma kuma hakan bai hana shi shan kaye ba.

Shi dai Bashir ya zargi shugabannin jam’iyyar a jihar da yin masa magudi a zaben, inda ya yi zargin an yi amfani da ‘yan daba a kansa da kuma magoya bayansa wajen tursasa musu barin wurin zaben.

Masu saka ido a zaben sun bayyana cewa bayan rashin gogewa a siyasar mazaba, babban abin da ya sa mutanen Buhari suka sha kaye shi ne, shugaban kasa bai nuna sha’awa a cikin takararsu ba.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

Next Post

Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Related

Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Amanna Da Jam’iyyun Siyasa – Akpabio

14 hours ago
Jega Ga Tinubu: Ka Sake Duba Nadin Kwamishinonin Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

Jega Ga Tinubu: Ka Sake Duba Nadin Kwamishinonin Zabe

7 days ago
Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello
Tambarin Dimokuradiyya

Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello

1 week ago
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”
Tambarin Dimokuradiyya

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

2 weeks ago
Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

2 weeks ago
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa – Buhari

2 weeks ago
Next Post
Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Jam'iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

December 8, 2023
Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

December 8, 2023
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

December 8, 2023
Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

Kasar Sin Ta Wallafa Wani Shiri Don Inganta Yanayin Iska

December 8, 2023
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

December 8, 2023
Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba

Sinawa: Mutane Masu Kwazo Da Girmama Baki Da Ke Kallon Alkiblar Kawo Ci Gaba

December 8, 2023
Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba

Sin: Matakan Kuntatawa Na Kasar Amurka Kan Kasar Sin Ba Zai Hana Bunkasuwar Sin Ba

December 8, 2023
Gwamna Yusuf

Gwamnan Kano Zai Gana Da Shugaban ‘Yan Fansho Kan Batan Naira Biliyan 5

December 8, 2023
Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

December 8, 2023
Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

December 8, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.