ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Buhari

Tsofaffin mataimaka na musamman ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wadanda suka tsaya takara a jam’iyyar APC na neman kujerar gwamna da majalisar dattawa da na majalisar wakilai a Jihar Kano dukkan su sun sha kaye a zaben fitar da gwani.

Sun dai hada da Sha’aban Sharada, wanda shi ne tsohon mataimaki na musam-man ga shugaban kasa kan watsa labarai, wanda a halin yanzu haka shi ne shuga-ban kwamitin majalisar wakilai kan fasahar tsaron kasa da tsohon mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai na zamani, Bashir Ahmad da kuma tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan bunkasa zamantakewa, Ismaeel Ahmed duk sun sha kaye a zaben fitar da gwani da ya gabata a Jihar Kano.

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Ba Da Kyauta Ga Daliban Ghana Da Ke Fama Da Talauci

Sun dai sha kayen ne a hannun ‘yan takarar da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mara wa baya.

ADVERTISEMENT

Shi dai Sha’aban ya tsaya takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar, yayin da Bashir ya nemi samun tikitin takarar dan majalisa na mazanar Albasu/Gaya/Ajingi, sai kuma Ismaeel da ya nemi tikitin takarar dan majalisar dattawa na Kano ta tsakiya.

Ismaeel ya bayyana janyewar takararsa mintina kadan kafin gudanar da zaben fitar da gwani. Amma shi Sha’aban da kuma Bashir an gudanar da zaben fitar da gwanin da su wadanda suka sha kaye.
Bayanai dai sun nuna cewa, Ismaeel ya janye takararsa ne bayan da gwamna ya tabbatar masa da cewa Abdulsalam Abdulkarim Zaura zai bai wa tikitin takara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sha’aban dai ya samu kuri’u 30, yayin da abokin karawarsa mataimakin gwamna, Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya lashe zaben ya samu kuri’u 2,289.

Bashir dai ya samu kuri’a 16, yayin da abokin karawarsa da ya lashe zaben, Abdul-lahi Mahmoud Gaya ya samu kuri’u 109.

Masu sharhi kan zaben Kano sun bayyana cewa sakamakon zaben fitar da gwani na takarar gwamnan bai zo da mamaki ba, saboda Sha’aban yana takun-saka da gwamna da kuma shugabannin jam’iyyar APC na jihar tun a shekarar 2021.

Shi kuma Bashir a tunaninsa zai iya samun tikitin takarar dan majalisar wakilai ci-kin ruwan sanyi tun da dai ya kasance yaro ne ga fadar shugaban kasa kamar dai abokinsa Sha’aban, amma bai yi nasara ba.

Majiyar ta tabbatar da cewa, lokacin da Bashir ya bayyana wa shugaban kasa a niyarsa ta tsayawa takara ya amince da bukatarsa kamar dai sauran ‘yan takara da suka bayyana masa aniyarsu. Amma kuma hakan bai hana shi shan kaye ba.

Shi dai Bashir ya zargi shugabannin jam’iyyar a jihar da yin masa magudi a zaben, inda ya yi zargin an yi amfani da ‘yan daba a kansa da kuma magoya bayansa wajen tursasa musu barin wurin zaben.

Masu saka ido a zaben sun bayyana cewa bayan rashin gogewa a siyasar mazaba, babban abin da ya sa mutanen Buhari suka sha kaye shi ne, shugaban kasa bai nuna sha’awa a cikin takararsu ba.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Jam’iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Jam'iyyar ZLP Ta Tsayar Da Dan Takarar Gwamna A Jihar Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.