• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

by CMG Hausa
3 years ago
Zaman lafiya

An rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, bayan an sake zaben Xi Jinping a matsayin shugaban kasar Sin a wa’adi na uku, na shekaru 5.

Jawabin da shugaban ya yi a jiya, ya ja hankalina matuka, inda yake cewa, amincewa da shi da jama’a suka yi, ita ce ke ba shi kwarin gwiwar ci gaba da yin aiki, wanda babban nauyi ne da ya rataya a wuyansa.

  • Yankin Daji A Kasar Sin Ya Karu Da Kadada Miliyan 22 Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ba shakka, sirrin ci gaban kowacce kasa da ma tabbatuwar zaman lafiya a kasar, shi ne shugabanci na gari. Kuma sai shugaba ya zama nagartacce kafin al’umma su aminta da shi.

Jagorantar mutanen da yawansu ya kai biliyan 1.4, ba karamin abu ba ne. Hausawa kan ce idan dambu ya yi yawa, to ba ya jin mai. Sai dai wannan zance ya sha bambam da yanayin kasar Sin, domin an ga yadda al’ummar kasar da ta zarce yawan na kowacce kasa a duniya, ke rayuwa cikin kwanciyar hankali da lumana da wadata, haka kuma sun kasance masu matukar biyayya ga shugabanninsu tare da amincewa da manufofin da suka gabatar.

Karkashin jagorancin Xi Jinping, kasar Sin ta samu muhimman nasarori da ba a taba gani ba a tarihi, lamarin da jagorancin al’ummar kasar shiga wani sabon babi na ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Misali, a karkashin shugabancinsa ne kasar Sin ta yi adabo da talauci baki daya, shekaru 10 kafin ma lokacin da MDD ke fata. Haka kuma, jama’ar kasar na more zaman lafiya da kwanciyar hankali da zaman jituwa tsakanin mabanbantan kabilu dake akwai. An kuma ga yadda kasar Sin da ba ta da yawan filayen noma, take iya ciyar da al’ummarta har ma take bayar da gudunmawar abinci ga masu bukata, baya ga yadda kasar ta kai matsayin koli wajen jagorantar duniya a fannonin fasahohin zamani da tattalin arziki da sauransu.

Shugaban ya kara da cewa, zai sadaukar da kansa, kuma zai yi aiki tukuru bisa bukatun kasa, da muradun jama’a. A ganina, shugaba kasar Sin ya riga ya cika burin al’umma da muradinsu, shi ya sa suka aminta da shi, suke ba shi goyon baya, tare da kara ba shi ragamar mulkin kasar. Ba makawa alkwarin nan da ya yi musu, zai cika shi kamar yadda aka gani a baya.

Hakika sake zabensa da Sinawa suka yi, ya tabbatar da cewa, suna son ci gaba da more rayuwa ta jin dadi da sauran al’ummomin duniya ke muradi. Haka kuma, wannan ya tabbatar wa duniya cewa, salon demokuradiyyar kasar Sin, demokradiyya ce ta al’umma domin al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
Daga Birnin Sin

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera
Daga Birnin Sin

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana
Daga Birnin Sin

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Next Post
Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

LABARAI MASU NASABA

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025
Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

October 22, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.