ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

by CMG Hausa
3 years ago
Zaman lafiya

An rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, bayan an sake zaben Xi Jinping a matsayin shugaban kasar Sin a wa’adi na uku, na shekaru 5.

Jawabin da shugaban ya yi a jiya, ya ja hankalina matuka, inda yake cewa, amincewa da shi da jama’a suka yi, ita ce ke ba shi kwarin gwiwar ci gaba da yin aiki, wanda babban nauyi ne da ya rataya a wuyansa.

  • Yankin Daji A Kasar Sin Ya Karu Da Kadada Miliyan 22 Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ba shakka, sirrin ci gaban kowacce kasa da ma tabbatuwar zaman lafiya a kasar, shi ne shugabanci na gari. Kuma sai shugaba ya zama nagartacce kafin al’umma su aminta da shi.

ADVERTISEMENT

Jagorantar mutanen da yawansu ya kai biliyan 1.4, ba karamin abu ba ne. Hausawa kan ce idan dambu ya yi yawa, to ba ya jin mai. Sai dai wannan zance ya sha bambam da yanayin kasar Sin, domin an ga yadda al’ummar kasar da ta zarce yawan na kowacce kasa a duniya, ke rayuwa cikin kwanciyar hankali da lumana da wadata, haka kuma sun kasance masu matukar biyayya ga shugabanninsu tare da amincewa da manufofin da suka gabatar.

Karkashin jagorancin Xi Jinping, kasar Sin ta samu muhimman nasarori da ba a taba gani ba a tarihi, lamarin da jagorancin al’ummar kasar shiga wani sabon babi na ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Misali, a karkashin shugabancinsa ne kasar Sin ta yi adabo da talauci baki daya, shekaru 10 kafin ma lokacin da MDD ke fata. Haka kuma, jama’ar kasar na more zaman lafiya da kwanciyar hankali da zaman jituwa tsakanin mabanbantan kabilu dake akwai. An kuma ga yadda kasar Sin da ba ta da yawan filayen noma, take iya ciyar da al’ummarta har ma take bayar da gudunmawar abinci ga masu bukata, baya ga yadda kasar ta kai matsayin koli wajen jagorantar duniya a fannonin fasahohin zamani da tattalin arziki da sauransu.

Shugaban ya kara da cewa, zai sadaukar da kansa, kuma zai yi aiki tukuru bisa bukatun kasa, da muradun jama’a. A ganina, shugaba kasar Sin ya riga ya cika burin al’umma da muradinsu, shi ya sa suka aminta da shi, suke ba shi goyon baya, tare da kara ba shi ragamar mulkin kasar. Ba makawa alkwarin nan da ya yi musu, zai cika shi kamar yadda aka gani a baya.

Hakika sake zabensa da Sinawa suka yi, ya tabbatar da cewa, suna son ci gaba da more rayuwa ta jin dadi da sauran al’ummomin duniya ke muradi. Haka kuma, wannan ya tabbatar wa duniya cewa, salon demokuradiyyar kasar Sin, demokradiyya ce ta al’umma domin al’umma.

Zaman lafiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.