ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

by CMG Hausa
3 years ago
Zaman lafiya

An rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, bayan an sake zaben Xi Jinping a matsayin shugaban kasar Sin a wa’adi na uku, na shekaru 5.

Jawabin da shugaban ya yi a jiya, ya ja hankalina matuka, inda yake cewa, amincewa da shi da jama’a suka yi, ita ce ke ba shi kwarin gwiwar ci gaba da yin aiki, wanda babban nauyi ne da ya rataya a wuyansa.

  • Yankin Daji A Kasar Sin Ya Karu Da Kadada Miliyan 22 Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ba shakka, sirrin ci gaban kowacce kasa da ma tabbatuwar zaman lafiya a kasar, shi ne shugabanci na gari. Kuma sai shugaba ya zama nagartacce kafin al’umma su aminta da shi.

ADVERTISEMENT

Jagorantar mutanen da yawansu ya kai biliyan 1.4, ba karamin abu ba ne. Hausawa kan ce idan dambu ya yi yawa, to ba ya jin mai. Sai dai wannan zance ya sha bambam da yanayin kasar Sin, domin an ga yadda al’ummar kasar da ta zarce yawan na kowacce kasa a duniya, ke rayuwa cikin kwanciyar hankali da lumana da wadata, haka kuma sun kasance masu matukar biyayya ga shugabanninsu tare da amincewa da manufofin da suka gabatar.

Karkashin jagorancin Xi Jinping, kasar Sin ta samu muhimman nasarori da ba a taba gani ba a tarihi, lamarin da jagorancin al’ummar kasar shiga wani sabon babi na ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Misali, a karkashin shugabancinsa ne kasar Sin ta yi adabo da talauci baki daya, shekaru 10 kafin ma lokacin da MDD ke fata. Haka kuma, jama’ar kasar na more zaman lafiya da kwanciyar hankali da zaman jituwa tsakanin mabanbantan kabilu dake akwai. An kuma ga yadda kasar Sin da ba ta da yawan filayen noma, take iya ciyar da al’ummarta har ma take bayar da gudunmawar abinci ga masu bukata, baya ga yadda kasar ta kai matsayin koli wajen jagorantar duniya a fannonin fasahohin zamani da tattalin arziki da sauransu.

Shugaban ya kara da cewa, zai sadaukar da kansa, kuma zai yi aiki tukuru bisa bukatun kasa, da muradun jama’a. A ganina, shugaba kasar Sin ya riga ya cika burin al’umma da muradinsu, shi ya sa suka aminta da shi, suke ba shi goyon baya, tare da kara ba shi ragamar mulkin kasar. Ba makawa alkwarin nan da ya yi musu, zai cika shi kamar yadda aka gani a baya.

Hakika sake zabensa da Sinawa suka yi, ya tabbatar da cewa, suna son ci gaba da more rayuwa ta jin dadi da sauran al’ummomin duniya ke muradi. Haka kuma, wannan ya tabbatar wa duniya cewa, salon demokuradiyyar kasar Sin, demokradiyya ce ta al’umma domin al’umma.

Zaman lafiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

Chelsea Za Ta Shirya Wa Musulmi Shan Ruwa A Watan Ramadan 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.