• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

by Muhammad
6 months ago
in Labarai
0
SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyar Ci gaban Kasuwar Singa da ke Kano a karkashin Jagorancin Shugaban ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari da Shugaban Dattijan Ƙungiyar kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, sun karɓi baƙuncin tawagar wakilan Jami’ar Skyline da ke Kano a ranar Alhamis 16, ga watan Janairun 2025 a ofishin Sambajo da ke Kasuwar Singa Kano.

Tawagar wakilan Jami’ar Skyline ta kawo ne ziyarar ne a ƙarƙashin jagorancin uban Jami’ar, Mista Nitin Anand da Daraktan Jami’ar, Abubakar Sadik Isma’il.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Babbban makasudin kawo shi ne sanya albarka daga Shugaban Dattijan Kungiyar SIMDA, Alhaji Salisu Sambajo da ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ƙungiyar SIMDA kan bunkasa harkokin kasuwanci da ilimi a jihar Kano.

A jawabin Mista Anand na Jami’ar Skyline ya ce, su na neman tabarrakin Alhaji Salisu Sambajo da ƙungiyar SIMDA da kuma neman ta su gudunmawar wajen bunkasa harkokin Jami’ar da ɓangaren ilimi da kasuwanci a Kano.

Ya kuma yi alkawarin bai wa shugabancin ƙungiyar SIMDA ragin kuɗaɗen shiga makarantar da kashi 50 cikin kashi 100 kan duk ɗalibin da Kungiyar ta dauki nauyin bai wa tallafin karatu a jami’ar, sannan Jami’ar za ta bai wa mambobin Kasuwar Singa bita da horo na yini guda kyauta da kuma ba su takardar shaidar horo a kan kasuwancin zamani a matsayin wani bangare na tukuici ga ƙungiyar ta SIMDA.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

A jawabin dattijon Ƙungiyar SIMDA kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, ya bayyana farin cikinsa da jin daɗi kan kawo ziyarar wakilan Jami’ar, ya kuma yi alƙawarin bayar da duk wata gudunmowa da za ta kyautata alaƙa kan ci gaban ilimi da kasuwanci a tsakanin ƙungiyar SIMDA da Jami’ar.

Shugaban Ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari, ya gode wa wakilan Jami’ar bisa karrama su da su ka yi wajen kawo ziyarar, ya kuma ce su ma za su kai musu makamanciyar ziyarar don kara karfafa zumunci da tattaunawa kan yadda za a bunƙasa ɓangaren ilimi da kasuwanci a kasuwar.

Barista Junaidu ya ce, za su duba hanyoyin da za su bi don bayar da ta su gudunmawar a ƙungiyance.

Shugaban ya kuma gode wa Jami’ar kan horo da bitar da Jami’ar za ta shirya wa mambobin ƙungiyar na kasuwar Singa.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin shugabanin ƙungiyar da mambobinta da sauransu.

SIMDA

SIMDA SIMDA SIMDA


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊalibaiJami'akanoƘungiyaSinga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Next Post

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

4 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

8 hours ago
Next Post
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan 'Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.