• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

A yau, al’ummar kasar Sin sun gudanar da wani gagarumin gangami da faretin soji a birnin Beijing na kasar, domin tunawa da cikar shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Shugabanin wasu kasashe 26 ne suka halarci bikin tunawa da ya gudana, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin cewa, jama’ar kasar Sin za su tsaya tsayin daka wajen bin tafarki na gaskiya, wanda zai haifar da ci gaban daukacin dan Adam, da bin hanyar raya kasa cikin lumana, da yin aiki kafada da kafada da al’ummun kasashe daban daban, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama.

 

Me ya sa Sinawa za su iya bin tafarki na gaskiya? Domin sun dade suna jin radadin yake-yake.

  • Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
  • Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Kasar Sin babban fagen daga ne a yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Lokacin da sojojin Japan suka fara mamaye kasar Sin a shekara ta 1931, Sinawa sun kasance na farko a duniya wajen daga tutar yaki da tafarkin murdiya. Yayin da wasu kasashen yammacin duniya ke tunanin magance yaki da ‘yan Nazi, sojoji da fararen hula na kasar Sin sun riga sun tashi haikan don yaki da maharan kasar Japan, ko da yake ba su da makamai masu inganci a lokacin.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, kasar Sin ta kasance cikin talauci da rauni, kuma sadaukarwar da Sinawa suka yi wajen kare kasarsu tana da yawa. Bisa kididdigar da aka yi, yawan sojojin kasar Sin da fararen hula na kasar da suka rasa rayuka, ko kuma suka ji rauni a yakin da suka yi da sojojin Japan ya zarce miliyan 35, inda yawan hasarar da aka samu ya haura dala biliyan 600. Al’ummar kasar Sin, bisa babbar sadaukarwar da suka yi, sun samar da damar cin nasara a yakin da jama’ar kasashe daban daban suka yi na kin tafarkin murdiya. Saboda a yayin yakin na tsawon shekaru 14 da Sinawa suka yi da maharan kasar Japan, fagen daga dake kasar Sin ya janyo hankalin kaso 60% zuwa 94% na sojojin kasa na kasar Japan. Wannan yanayi ya wargaza muradin sojojin Japan da masu bin tafarkin murdiya na kasar Jamus, na hadin gwiwa a kokarin mamaye duniya daga dukkan bangarorin gabas da yamma.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Yakin da Sinawa suka yi cikin adalci ya sa su samun karramawa, da goyon baya daga gamayyar kasa da kasa. Kana yadda al’ummun kasashe daban daban a wancan lokaci suka hada kai da juna a karkashin tutar yaki da tafarkin murdiya, ko da yake akwai bambanci a tsakaninsu ta fuskokin kasa, da kabila, da kuma akida, ya kai ga cimma nasara a yakin kin tafarkin murdiya, da tabbatar da sabon tsarin kasa da kasa bayan yakin a karshe.

Tarihin yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya ya nuna mana wasu tunani masu zurfi, wadanda jama’ar kasar Sin suka san su sosai:

Da farko dai, komai wahalhalun da aka sha, adalci zai yi galaba a kan muguntawa, haske kuma zai kori duhu. Wannan tamkar doka ce ta tarihi.

Na biyu, ‘yan Adam na da makomar bai daya. Ya kamata a samu daidaituwa, da jituwa, da cude-ni-in-cude-ka, tsakanin kasashe da kabilu daban daban, ta yadda za a samu damar tabbatar da tsaron bai daya, da kawar da yaki daga karshensa.

A zamanin da muke ciki, ana ta samun abkuwar rikice-rikice a duniya, inda dan Adam suka sake fuskantar bukatar yin zabi tsakanin cudanya da juna ko yin gaba da juna, zaman lafiya ko yaki. Sai dai kasar Sin ta riga ta samu babban ci gaba: Yanzu kasar na bikin tunawa da nasarar da ta samu ta gagarumin faretin soji. Kana a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, jama’ar kasar na ta kokarin zamanantar da kasarsu bisa hadin kansu.

Jawabin shugaba Xi Jinping ya bayyanawa duniya cewa: Kasar Sin mai karfi za ta ci gaba da samar da gudummawa ga ci gaban al’ummar dan Adam da na tattalin arzikin duniya cikin lumana.

Bari mu yi kokarin neman samun ci gaba tare, bisa wani tafarki na gaskiya. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.