• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Maraba Da Karin Baki Da Su Yi Dadin Yawon Bude Ido A Kasar

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Maraba Da Karin Baki Da Su Yi Dadin Yawon Bude Ido A Kasar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na maraba da karin abokai ‘yan yawon bude ido, dake son zuwa kashe kwarkwatar ido a dukkanin sassan kasar, da wurare masu kayatarwa dake cikin kasar.

Lin Jian, ya bayyana hakan ne a Larabar nan, lokacin da yake tsokaci game da yadda ziyarar rukunin jama’a ke kara samun karbuwa a kasuwannin yawon bude ido na kasa da kasa.

  • Fahimtar Manufar Kasar Sin Ta Yin Kwaskwarima A Sabon Zamani: Lafiyar Al’umma Shi Ne Tushen Zaman Lafiyar Kasa
  • IMF Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2024 Zuwa Kashi 5%

Rahotanni na cewa, a baya-bayan nan, ana matukar kara samun masu sha’awar ziyartar kasar Sin domin yawon shakatawa, wanda hakan wani tagomashi ne da Sin din ke samu a kasuwannin yawon bude ido na kasa da kasa. Wasu kamfanonin shirya tafiye-tafiye na kasa da kasa ma na cewa a bana, adadin baki ‘yan kasashen waje dake neman ziyartar kasar Sin ya linka har rubi 4 kan na shekarar bara.

Game da hakan, Lin Jian ya ce Sin na ci gaba da goyon bayan harkokin musayar jama’a tsakaninta da takwarori na kasashen waje, inda al’ummun kasashe 15 irinsu Faransa, suka shiga tsarin gwajin ziyartar kasar Sin ba tare da Biza ba na tsawon kwanaki 15, kana Sin ta fadada aiwatar da tsarin ba da izinin yada zango ba tare da Biza ba, har na tsawon sa’o’i 144 ga al’ummun wasu kasashe, a wasu tasoshin shiga kasar ta Sin da aka kara adadinsu zuwa 37.

Tuni dai kasar Sin ta fara aiwatar da cikakken tsarin shiga ba Biza, ga baki masu yawon bude ido na rukunonin jama’a, wadanda suke cikin jiragen ruwa na yawon shakatawa, kana tana aiwatar da tsarin kyautata hidimomi masu nasaba da hakan, irinsu biyan kudade ta wayar salula, da sayen tikiti a wuraren da suke ziyarta cikin kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nada Didi Walson-Jack A Matsayin Sabuwar Shugabar Ma’aikata

Next Post

Yancin Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi: Zamu Sa Ido Kan Tafiyar Da Kuɗaɗen Al’umma – Dikko Raɗɗa 

Related

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

22 minutes ago
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

1 hour ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

2 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

3 hours ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

4 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

13 hours ago
Next Post
katsina

Yancin Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi: Zamu Sa Ido Kan Tafiyar Da Kuɗaɗen Al'umma - Dikko Raɗɗa 

LABARAI MASU NASABA

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

August 7, 2025
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.