ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Maraba Da Karin Baki Da Su Yi Dadin Yawon Bude Ido A Kasar

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na maraba da karin abokai ‘yan yawon bude ido, dake son zuwa kashe kwarkwatar ido a dukkanin sassan kasar, da wurare masu kayatarwa dake cikin kasar.

Lin Jian, ya bayyana hakan ne a Larabar nan, lokacin da yake tsokaci game da yadda ziyarar rukunin jama’a ke kara samun karbuwa a kasuwannin yawon bude ido na kasa da kasa.

  • Fahimtar Manufar Kasar Sin Ta Yin Kwaskwarima A Sabon Zamani: Lafiyar Al’umma Shi Ne Tushen Zaman Lafiyar Kasa
  • IMF Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2024 Zuwa Kashi 5%

Rahotanni na cewa, a baya-bayan nan, ana matukar kara samun masu sha’awar ziyartar kasar Sin domin yawon shakatawa, wanda hakan wani tagomashi ne da Sin din ke samu a kasuwannin yawon bude ido na kasa da kasa. Wasu kamfanonin shirya tafiye-tafiye na kasa da kasa ma na cewa a bana, adadin baki ‘yan kasashen waje dake neman ziyartar kasar Sin ya linka har rubi 4 kan na shekarar bara.

ADVERTISEMENT

Game da hakan, Lin Jian ya ce Sin na ci gaba da goyon bayan harkokin musayar jama’a tsakaninta da takwarori na kasashen waje, inda al’ummun kasashe 15 irinsu Faransa, suka shiga tsarin gwajin ziyartar kasar Sin ba tare da Biza ba na tsawon kwanaki 15, kana Sin ta fadada aiwatar da tsarin ba da izinin yada zango ba tare da Biza ba, har na tsawon sa’o’i 144 ga al’ummun wasu kasashe, a wasu tasoshin shiga kasar ta Sin da aka kara adadinsu zuwa 37.

Tuni dai kasar Sin ta fara aiwatar da cikakken tsarin shiga ba Biza, ga baki masu yawon bude ido na rukunonin jama’a, wadanda suke cikin jiragen ruwa na yawon shakatawa, kana tana aiwatar da tsarin kyautata hidimomi masu nasaba da hakan, irinsu biyan kudade ta wayar salula, da sayen tikiti a wuraren da suke ziyarta cikin kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
Daga Birnin Sin

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Next Post
katsina

Yancin Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi: Zamu Sa Ido Kan Tafiyar Da Kuɗaɗen Al'umma - Dikko Raɗɗa 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.