• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Muhalli shi ne rayuwa, dukkan halittu na bukatar kyautatuwar muhalli domin samun rayuwa mai inganci da walwala.

A yayin da aka gudanar da bikin ranar muhalli ta kasa da kasa a karshen wannan mako, masu ruwa da tsaki suna ci gaba da jaddada muhimmancin kare muhalli da yin kiraye-kirayen a kaucewa gurbata muhallin halittu, domin samun rayuwa mai inganci gami da kaucewa shiga mawuyacin hali a sakamakon gurbacewar muhallin.

A jawabin da ya gabatar a jajiberin bikin muhalli na shekarar 2022, babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya ce ana bukatar abubuwa masu tarin yawa a wannan duniyar tamu domin tafiyar da rayuwarmu yadda ya kamata, kuma abubuwan dake lalata muhalli ba kawai suna cutar da duniya ba ne, har ma da halittun dake rayuwa cikinta. An yi kiyasin sama da mutane biliyan 3 ne matsalolin tabarbarewar muhallin halittu ya shafa a duniya. Kana gurbacewar muhalli yana sanadiyyar mutuwar wuri na kusan mutane miliyan 9 a duk shekara a duniya, sannan sama da nau’ikan dabbobi da tsarrai miliyan 1 ne ke fuskantar barazanar bacewa daga doron kasa a duk shekara a duniya, kamar yadda babban jami’in MDDr ya bayyana. Ya ce nan da shekarar 2050, sama da mutane miliyan 200 ne a duk shekara za su fuskanci barazanar barin muhallansu sakamakon matsalolin sauyin yanayi.

Bisa lura da girman matsalolin da duniya ke fuskanta, ya sa mahukuntan kasar Sin ke tsayawa tsayin daka, wajen sauke nauyin dake bisa wuyansu na kare muhalli a mataki na cikin gida har ma da matakin kasa da kasa.

Matakan da kasar Sin ke dauka wajen kare muhalli ya yi matukar daukar hankalin kasa da kasa, kamar yadda Elizabeth Maruma Mrema, babbar sakatariyar sashen kula da nau’ikan halittu ta MDD ta ce, kasar Sin ta cimma muhimman sakamako masu karfafa gwiwa a fannonin yaki da matsalar sauyin yanayi, da kandagarkin bacewar nau’in halittu, da rage iska mai gurbata muhalli. Mrema ta yi wannan tsokaci ne a lokacin bikin ranar kare muhalli ta kasar Sin ta shekarar 2022, inda ta bayyana hakan a jawabin da ta gabatar. Taken bikin na bana shi ne, “mu yi aiki tare don gina kyakkyawar duniya mai tsafta.” Jami’ar MDD ta ce, kasar Sin ta yi aiki tukuru, tare da bayar da gagarumar gudunmawa ga kokarin da duniya ke yi wajen magance matsalolin dake shafar muhalli, da daga matsayin aikin gina cigaba mai dorewa, da kuma gina makomar al’umma don kyautata rayuwar dukkan bil adama a duniya. Bugu da kari, ta kuma yabawa matakan da kasar Sin ke dauka wajen kiyaye nau’ikan halittu, matakan da suka hada da kafa lambunan shan iska na kasa, da kuma samar da dokokin dake shafar kiyaye muhallin halittu. Guterres ya bukaci gwamnatoci da su bada fifiko wajen daukar matakan tinkarar matsalolin sauyin yanayi, da kare muhalli, ta hanyar bullo da manufofin da zasu taimaka wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cikin wasikar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike don taya murna bikin ranar muhalli ta kasar Sin na shekarar 2022, ya yi nuni da cewa, muhallin halittu shi ne ginshikin rayuwa da ci gaban dan Adam, kuma kiyaye muhalli yadda ya kamata shi ne burin bai daya na jama’ar kasashe daban daban. Ya ce tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, kasar Sin ta dauki aikin raya al’adun halittu a matsayin wani muhimmin shiri mai alaka da samun dauwamammen ci gaban al’ummar kasar, tana kuma tsayawa kan ra’ayinta na “tabbatar da kyakkyawan muhalli shi ne arzikinmu”.

Ranar muhalli ta duniya, ta kasance a matsayin wani muhimmin lokaci da MDD ke amfani da shi, wajen fadakar da duniya game da matakan da suka dace a dauka don kare muhalli. (Ahmad Fagam)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

Next Post

Rahoton Shekara-shekara Kan ‘Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma’auni Biyu Da Take Dauka

Related

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

58 minutes ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

2 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

3 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

1 day ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

1 day ago
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

1 day ago
Next Post
Rahoton Shekara-shekara Kan ‘Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma’auni Biyu Da Take Dauka

Rahoton Shekara-shekara Kan 'Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma'auni Biyu Da Take Dauka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.