• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Muhalli shi ne rayuwa, dukkan halittu na bukatar kyautatuwar muhalli domin samun rayuwa mai inganci da walwala.

A yayin da aka gudanar da bikin ranar muhalli ta kasa da kasa a karshen wannan mako, masu ruwa da tsaki suna ci gaba da jaddada muhimmancin kare muhalli da yin kiraye-kirayen a kaucewa gurbata muhallin halittu, domin samun rayuwa mai inganci gami da kaucewa shiga mawuyacin hali a sakamakon gurbacewar muhallin.

A jawabin da ya gabatar a jajiberin bikin muhalli na shekarar 2022, babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya ce ana bukatar abubuwa masu tarin yawa a wannan duniyar tamu domin tafiyar da rayuwarmu yadda ya kamata, kuma abubuwan dake lalata muhalli ba kawai suna cutar da duniya ba ne, har ma da halittun dake rayuwa cikinta. An yi kiyasin sama da mutane biliyan 3 ne matsalolin tabarbarewar muhallin halittu ya shafa a duniya. Kana gurbacewar muhalli yana sanadiyyar mutuwar wuri na kusan mutane miliyan 9 a duk shekara a duniya, sannan sama da nau’ikan dabbobi da tsarrai miliyan 1 ne ke fuskantar barazanar bacewa daga doron kasa a duk shekara a duniya, kamar yadda babban jami’in MDDr ya bayyana. Ya ce nan da shekarar 2050, sama da mutane miliyan 200 ne a duk shekara za su fuskanci barazanar barin muhallansu sakamakon matsalolin sauyin yanayi.

Bisa lura da girman matsalolin da duniya ke fuskanta, ya sa mahukuntan kasar Sin ke tsayawa tsayin daka, wajen sauke nauyin dake bisa wuyansu na kare muhalli a mataki na cikin gida har ma da matakin kasa da kasa.

Matakan da kasar Sin ke dauka wajen kare muhalli ya yi matukar daukar hankalin kasa da kasa, kamar yadda Elizabeth Maruma Mrema, babbar sakatariyar sashen kula da nau’ikan halittu ta MDD ta ce, kasar Sin ta cimma muhimman sakamako masu karfafa gwiwa a fannonin yaki da matsalar sauyin yanayi, da kandagarkin bacewar nau’in halittu, da rage iska mai gurbata muhalli. Mrema ta yi wannan tsokaci ne a lokacin bikin ranar kare muhalli ta kasar Sin ta shekarar 2022, inda ta bayyana hakan a jawabin da ta gabatar. Taken bikin na bana shi ne, “mu yi aiki tare don gina kyakkyawar duniya mai tsafta.” Jami’ar MDD ta ce, kasar Sin ta yi aiki tukuru, tare da bayar da gagarumar gudunmawa ga kokarin da duniya ke yi wajen magance matsalolin dake shafar muhalli, da daga matsayin aikin gina cigaba mai dorewa, da kuma gina makomar al’umma don kyautata rayuwar dukkan bil adama a duniya. Bugu da kari, ta kuma yabawa matakan da kasar Sin ke dauka wajen kiyaye nau’ikan halittu, matakan da suka hada da kafa lambunan shan iska na kasa, da kuma samar da dokokin dake shafar kiyaye muhallin halittu. Guterres ya bukaci gwamnatoci da su bada fifiko wajen daukar matakan tinkarar matsalolin sauyin yanayi, da kare muhalli, ta hanyar bullo da manufofin da zasu taimaka wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Cikin wasikar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike don taya murna bikin ranar muhalli ta kasar Sin na shekarar 2022, ya yi nuni da cewa, muhallin halittu shi ne ginshikin rayuwa da ci gaban dan Adam, kuma kiyaye muhalli yadda ya kamata shi ne burin bai daya na jama’ar kasashe daban daban. Ya ce tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, kasar Sin ta dauki aikin raya al’adun halittu a matsayin wani muhimmin shiri mai alaka da samun dauwamammen ci gaban al’ummar kasar, tana kuma tsayawa kan ra’ayinta na “tabbatar da kyakkyawan muhalli shi ne arzikinmu”.

Ranar muhalli ta duniya, ta kasance a matsayin wani muhimmin lokaci da MDD ke amfani da shi, wajen fadakar da duniya game da matakan da suka dace a dauka don kare muhalli. (Ahmad Fagam)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

Next Post

Rahoton Shekara-shekara Kan ‘Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma’auni Biyu Da Take Dauka

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

5 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

6 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

7 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

8 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

9 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

11 hours ago
Next Post
Rahoton Shekara-shekara Kan ‘Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma’auni Biyu Da Take Dauka

Rahoton Shekara-shekara Kan 'Yancin Addinai Na Duniya, Yana Fallasa Munafuncin Amurka Da Ma'auni Biyu Da Take Dauka

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.