• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan barkewar sabon zagayen tashin hankali tsakanin Falasdinawa da dakarun Isra’ila, mutane sama da 11,000 sun rasa rayukansu a Gaza, wanda hakan ya yi matukar tada hankalin sassan kasa da kasa, kuma tuni kasashen duniya suka fara kiraye-kirayen ganin an gaggauta dakatar da bude wuta, tare da kawo karshen zubar da jini.

A bangaren sassa dake taka rawar gani wajen ganin an kawo karshen wannan tashin hankali, ko shakka babu kasar Sin ta yi fice, ganin yadda tun farkon lamarin mahukuntan take ta tattaunawa da sassan masu ruwa da tsaki, kaza lika Sin ta yi tsayin daka wajen tattaunawa da ragowar kasashen duniya karkashin kwamitin tsaron MDD, kana ta yi duk mai yiwuwa wajen ingiza dawo da zaman lafiya, da kai zuciya nesa, domin ganin an yayyafawa wutar tashin hankalin ruwa.

  • Sin Na Da Mutane Sama Da Miliyan 364 Dake Amfani Da Hidimomin Kiwon Lafiya Ta Yanar Gizo
  • Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

Bisa himma da kasar Sin ke yi, da mayar da hankali sosai kan wannan lamari, ta lura da manyan bukatun da ake da su na shawo kan lamarin, har ma ta gabatar da matsaya karkashin jigo 4.

Da farko dai kasar Sin na tsaye kan burin tabbatar da an kare mutuntaka, wato aiwatar da dukkanin matakai na kare hakkokin dan Adam na rayuwa, kamar dai yadda dokokin jin kai na kasa da kasa suka tanada. Na biyu kuwa, Sin ta yi amanar cewa, aiwatar da matakan siyasa ne kadai za su ba da damar kawo karshen yakin da ake gwabzawa tsakanin Falasdinawa da tsagin Isra’ila. Sai kuma na uku, wato cudanyar sassa daban daban, ta fannin shawarwari da aiwatar da matakan da suka dace, wanda zai taimaka matuka wajen ganin bayan wannan rikici. Sannan kuma na hudu, Sin ta yi imanin cewa, wajibi ne a magance tushe, da kuma abubuwan da suka haifar da wannan rikici wanda ke ta maimaituwa tsawon lokaci. Karkashin hakan, kasar Sin na ganin dole ne a tabbatar da kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, matakin da zai tabbatar da cikakken ’yancin Falasdinawa na samun kasarsu.

Idan mun yi la’akari na wadannan batutuwa da Sin ke tsaye a kansu, tabbas za mu gamsu da kyakkyawar manufar kasar, ta ganin an kawo karshen zubar jini tsakanin wadannan sassa biyu, da ma cimma burin ganin an bunkasa zaman lafiya da jituwa a gabas ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuGazaHamasIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Kutse Ta Intanet

Next Post

Bankin Jama’ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

38 minutes ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

2 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

3 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

4 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

5 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

24 hours ago
Next Post
Bankin Jama’ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

Bankin Jama'ar Sin: Fasahar Kudin Sin Na Sahun Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.