• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Damu Matuka Kan Ta’azzarar Rikici Da Tasirinsa Kan Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a yayin taron manema labaru na yau da kullum Alhamis din nan cewa, kasar Sin tana bakin ciki matuka da yadda rikicin da ke faruwa a halin yanzu tsakanin Palasdinu da Isra’ila, ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba, tare da nuna matukar damuwa game da tabarbarewar yanayin tsaro da ma jin kai a yankin Falasdinu, ta kuma damu matuka game da mummunan tasirin da tashin hankalin zai haifar ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Wang Wenbin ya bayyana cewa, kasar Sin ta lura cewa, kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta gudanar da taron gaggawa na ministocin harkokin wajen kungiyar, inda ta zartas da wani kuduri dake goyon bayan kungiyar wajen taka muhimmiyar rawa kan batun Palasdinu.

  • Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 
  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu

Kasar Sin da kasashen Larabawa na da kusan ra’ayi daya kan batun Falasdinu, inda bangarorin biyu suka yi kira da a hanzarta tsagaita bude wuta da kawo karshen hare-haren bama-bamai, da yin Allah wadai da ayyukan dake cutar da fararen hula, da kaucewa ta’azzarar al’amura da haddasa bala’in jin kai.

Wang Wenbin ya ce, kasar Sin tana son ci gaba da yin mu’amala da hadin gwiwa tare da dukkan bangarorin kungiyar hadin kan kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwarin zaman lafiya, da kokarin maido da shirin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya kan turba mai kyau.

Bugu da kari, a jiya manzon musamman na kasar Sin kan batun Gabas ta tsakiya Mr. Zhai Jun ya tattauna kan yanayin da Palestinu da Isra’ila ke ciki tare da mataimakiyar ministan harkokin wajen kasar Palestinu ta farko Amal Jadou ta wayar tarho, inda Zhai Jun ya bayyana cewa, kasar Sin ta damu matuka da rasuwar fararen hula da dama sakamakon rikicin Palestinu da Isra’ila.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Ya kara da cewa, yanzu abu mafi muhimmanci shi ne, a tsaigaita bude wuta nan take. Kuma kamata ya yi kasashen duniya su yi kokari domin sassauta rikicin, tare kuma da samar da taimakon jin kai ga al’ummar Palestinu. Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari domin cimma burin tsagaita bude wuta tsakanin sassan biyu, tare kuma da samar da tallafi domin sassauta rikicin jin kai, kana za ta ci gaba da shawo kan sassan biyu, su komawa shawarwarin wanzar da zaman lafiya, ta yadda za a daidaita batun Palestinu bisa adalci daga duk fannoni.

A na ta bangare, Jadou ta gode wa kasar Sin bisa matsayin adalcin da take kai game da batun Palestinu. A cewarta, Palestinu ta na da cikakken imani da kasar Sin, kuma tana fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka rawar gani kan batun a halin da ake ciki yanzu. (Mai fassara: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kasance Mai Asali Daga Sin Amma Mai Rungumar Dukkanin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.