Wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Fu Cong, ya gabatar da jawabi a gun taron muhawara mai taken “Talauci da karancin ci gaba da rikici”, wadda kwamitin sulhu na MDD ya gudanar a jiya Alhamis, inda ya ce matsalar fama da talauci, da rashin samun ci gaba, muhimman dalilai ne dake haifar da rikice-rikice, don haka ya kamata a yi hangen nesa, da tabbatar da shirin magance su baki daya.
Fu ya ce, “Dole ne mu taimakawa kasashe masu tasowa, ta yadda za su samu ci gaba, da mutunta hanyoyin da suka zaba na bunkasa bisa karfin kashin kansu, kana da zurfafa huldar abota ta hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa, da kuma ingiza kyautata tsarin daidaita harkokin duniya, da baiwa aikin wanzar da zaman lafiya a duniya muhimmanci.”
- Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
- Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
Jami’in ya kara da cewa, ya kamata kasashen duniya su gaggauta baiwa batun samun ci gaba muhimmancin gaske cikin ajandar kasa da kasa, ta yadda za a sanya batun rage talauci, da ba da ilmi, da tabbatar da samar da guraben aikin yi, da habaka karfin samun ci gaba da sauransu gaban komai, da kuma tabbatar da ba a bar kowa a baya ba.
Fu Cong ya kara da cewa, Sin ta gabatar da shawarar tsaron kasa da kasa, inda ta yi kira ga bangarori daban-daban na duniya, da su nacewa ra’ayin tsaro dake bukatar yin hadin gwiwa a dukkanin fannoni masu dorewa, matakin da ya gabatar da shiri iri na kasar Sin, ta fuskar warware rikice-rikice mafiya jawo hankali a siyasance.
Ya ce Sin tana iyakacin kokarinta, wajen shiga a dama da ita a sha’anin raya kasashen duniya baki daya, kuma tana hadin gwiwa da sauran kasashe, don tabbatar da nasarar ingantacciyar shawarar “ziri daya da hanya daya”, wanda hakan zai gaggauta ci gaban sassan kasa da kasa baki daya.
Kazalika, a cewar jami’in, Sin na kara bude kofarta ga ketare bisa matsayin koli, da shigo da jari cikin kasar a bangaren sana’o’in samar da kayayyaki, kana da yafe dukkannin harajin kwastam ga kasashen Afirka mafiya fama da karancin ci gaba da suka kulla dangantakar diplomasiyya da ita. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp