Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Geng Shuang ya yi jawabi a gun zaman shirya taron koli kan aiwatar da shirin kafa kasashe biyu a jiya Jumma’a 23 ga wannan wata cewa, aiki mafi muhimmanci da gaggawa shi ne tsagaita bude wuta da ceton rayukan jama’a a zirin Gaza.
Geng Shuang, ya bayyana cewa, kawo karshen rikici, tushe ne na shimfida zaman lafiya mai dorewa. Idan ba a cimma tsagaita bude wuta a zirin Gaza ba, tabbas shirin kafa kasashe biyu ba zai yi wani tasiri ba ko kadan.
A halin yanzu, kasar Isra’ila tana kara kai hare-haren kasa a zirin Gaza, da mamaye karin yankuna, hakan ya tsananta yanayin da ake ciki a zirin. Don haka, tilas ne kasa da kasa su yi namijin kokari wajen sa kaimi ga tsagaita bude wuta da sassauta yanayin jin kai a zirin Gaza, don kawo kyakkyawan fatan zaman rayuwa ga jama’ar zirin.
Kazalika, ya ce, kasar Sin ta nuna goyon bayan hada kan kasa da kasa ta hanyar gudanar da taron kolin, don nuna goyon baya ga Falasdinu da kuma aiwatar da shirin kafa kasashe biyu yadda ya kamata. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp