• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sirrin Ci Gaban Kasar Sin: Daga Yin Kwaskwarima Da Bude Kofa Zuwa Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru 45 da suka gabata, yawan kudin shigar kowa ne dan kasar Sin, dalar Amurka 190 ne kacal, wanda hakan ya sa ta kasance cikin kasashe mafi karancin ci gaba a duniya.

Jimillar yawan shigi da ficin kayayyaki, fiye da dalar Amurka biliyan 20 ne kawai, kuma amfani da jarin waje ba komai ba ne. Yayin da ake fuskantar irin wannan yanayi, shugaban Sin na lokacin Deng Xiaoping ya yanke shawarar aiwatar da manufar yin “gyare-gyare da bude kofa ga waje”. Mene ne gyare-gyare? Deng Xiaoping ya yi nuni da cewa, “gyare-gyare shi ne ‘yantar da sassan da suka dace.” Mene ne bude kofa? Deng Xiaoping ya ce, “Duniya a yau, duniya ce dake bude kofa, ba zai taba yiwuwa kowace kasa ta ci gaba da zama saniyar ware ba, idan har muna son samun bunkasuwa, tilas ne mu dage wajen bude kofa ga ketare.” A karkashin shawarar Deng Xiaoping, an rubuta shirin “yin gyare-gyare da bude kofa ga waje” cikin kundin tsarin mulkin kasar a matsayin muhimmin manufar kasar Sin.

  • Sin Tana Alfahari Da Yanayi Masu Kyau Don Jawo Jarin Waje
  • Kwamitin Tsaron MDD Ya Kada Kuri’a Kan Tsagaita Wuta A Gaza

Wannan manufa ta taimaka wajen inganta tsarin gurguzu mai sigar kasar Sin, ta kuma canza makomar kasar Sin ta zamani.

Shekaru 10 da suka gabata, a shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yanke shawarar zurfafa yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen waje. A cikin shekaru 10 da suka gabata, ta hanyar zurfafa yin gyare-gyare, kusan mutane miliyan 100 sun fita daga kangin fatara. A cikin shekaru 10 da suka gabata, kasar Sin ta gina tsarin masana’antu na zamani, da sa kaimi ga “juyin -juya hali”, da aiwatar da cikakken tsarin mulki bisa jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, da kuma yaki da cin hanci da rashawa, da kafa tsarin makomar Sin.

A shekarar 2022, kasar Sin ta bayyana cikakken zurfafa yin gyare-gyare a matsayin wani muhimmin abin da zai sa kasar Sin ta inganta hanyar zamanantarwa da farfado da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Kara zurfafa gyare-gyare a lokaci guda cikin sauri, shi ne babban matakin bude kofa ga kasashen waje. Xi ya yi imanin cewa, bude kofa yana kawo ci gaba, yayin da rufe kofa yana haifar da koma baya. A cikin shekaru 10 da suka gabata, Xi ya ba da shawarar yin hadin gwiwa wajen raya shawarar “Ziri daya da hanya daya”, kuma fiye da kasashe 150 da kungiyoyin kasa da kasa 30 sun rattaba hannu kan takardun hadin gwiwa fiye da 230.

Kasar Sin ta kafa yankuna ko tasoshin ruwa na ciniki cikin ‘yanci 23. Kasar Sin ta shirya bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin na farko a duniya, da baje kolin kayayyakin masarufi na kasa da kasa, da baje kolin inganta tsarin samar da kayayyaki na duniya.

Tun bayan da aka aiwatar da manufar yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen waje, yawan gudummawar da kasar Sin ta bayar ga ci gaban tattalin arzikin duniya, ya zarce kashi 30 cikin 100 cikin shekaru masu yawa.

Kasashen da suka ci gaba da masu tasowa, sun amfana matuka daga ci gaban tattalin arzikin kasar Sin, wanda hakan ya kara azama kan tattalin arzikin duniya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan siyasar AmurkaKasar SinTattalin Arzikin sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hausawan Ogun Na Zanga-zangar Neman Tabbatar Da Adalci A Shari’ar Gwamnan Kano

Next Post

NIS Reshen Ribas Ta Yi Wa Jami’ai Ado Da Sabbin Mukamai Da Kaddamar Da Sabbi

Related

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

8 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

12 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

13 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

14 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

15 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

15 hours ago
Next Post
NIS Reshen Ribas Ta Yi Wa Jami’ai Ado Da Sabbin Mukamai Da Kaddamar Da Sabbi

NIS Reshen Ribas Ta Yi Wa Jami’ai Ado Da Sabbin Mukamai Da Kaddamar Da Sabbi

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.