ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Armenia 50 Sun Mutu A Sabon Yakinsu Da Azerbaijan

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Kasar Armenia ta sanar da mutuwar kusan sojojinta 50 a sabon rikicin da ya barke tsakaninta da makwabciyarta Azerbaijan a ranar Talata, irinsa na farko tun bayan kazamin yakin da bangarorin biyu suka gwabza a shekarar 2020 gabanin kulla yarjejeniyar tsagaita wuta.

Bayan shafe tsawon dare ana gwabza yaki tsakanin dakarun bangarorin biyu da ya kai ga asarar dimbin rayuka, Armenia ta mika kokon barar neman taimako daga kasashen duniya don kange Azabaijan daga ci gaba da kutsawa cikin yankunanta da ke kan iyaka.

  • Burina Na Canza Rayuwar Al’umma Ta Hanyar Rubutu -Zahra Zamsarf
  • An Shiga Matakin Farfado Da Sassan Da Girgizar Kasa Ta Shafa A Lardin Sichuan

Kasashen biyu mambobin tsohuwar tarayyar Soviet tun bayan tsagaita wuta a yakin na 2020 daya kashe sojoji dubu 6 da 500 wannan mafi munin yaki da suka gwabza da juna duk dai kan yankin na Nagorno-Karabakh da ke kan iyakarsu.

ADVERTISEMENT

Tuni dai manyan kasashe suka fara tsoma baki a dadaddn rikicin, inda shugaba Vladimir Putin na Rasha ya tattaunawa da ministan harkokin wajen Armenia da nufin shiga tsakani don sasantawa yayin da a bangare guda shugaba Recep Tayyib Erdogan na Turkiyya ke gargadin kasashe da cewa kada su hasala Azerbaijan a kokarin nuna goyon bayansu ga Armenia.

Shi ma shugaba Emmanuel Macron na Faransa, yanzu haka na tattauna batun na Armenia a majalisar tsaron kasar don lalubo hanyar tallafawa kasar.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Firaministan Armenia Nikol Pashinyan, a jawabinsa gaban majalisar kasar a ranar Talata, ya ce yanzu haka dakarun kasar 49 suka rasa rayukansu a kan iyaka yayin da ya bai wa al’umma tabbacin samun taimako da kuma goyon baya daga Faransa da Rasha wadanda suka sha alwashin shiga tsakani.

Haka zalika yayin tattaunawar Firaministan da ministan harkokin wajen Amurka, Antony Blinken ya ba shi tabbacin shiga tsakani, yayin da ya roki kai zuciya nesa tsakanin kasashen biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Yi Watsi Da Karbar Albashi Mafi Tsoka A Duniya

Cristiano Ronaldo Ya Yi Watsi Da Karbar Albashi Mafi Tsoka A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.