ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Sojoji

Dakarun Bataliya ta daya Barikin Dukku da hadin guiwar ‘Yan banga a jihar kebbi sun yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su tare da fatattakar ‘yan bindiga da dama a dajin karamar hukumar Shanga da ke Jihar Kebbi.

Nasarar da aka samu ta biyo bayan wani aikin ceto da rundunar hadin guiwa da jami’an tsaro suka yi a dajin karamar hukumar Shanga bayan rahoton wadanda aka yi garkuwa da su.

  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Tare Da Gano Bindigar AK47 A Kebbi
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A cewar daraktan tsaro, AbdulRahman Usman, maza shidan da aka ceto duk sun kasance cikin koshin lafiya da kuma walwala da jin dadi kuma mayar da su cikin iyalansu.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa dakarun Bataliya ta 1 na Dukku Barrack da ke Birinin Kebbi da ke aikin share fage tare da hadin gwiwar ‘yan banga na yankin sun kai wani samame a tsaunin Kogon Damisa da ke kusa da Saminaka a karamar hukumar Shanga, wani gari mai iyaka tsakanin Kebbi da Jihar Neja.

A cewarsa, a yayin samamen, rundunar ta fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

“An ba da rahoton bacewar wadanda aka ceto, an yi garkuwa da su na dan wani lokaci, kafin samun nasarar ceto su.

An sanar da jami’an tsaro a yankin da suka hada da sojoji da ‘yan banga inda suka shiga cikin dajin Shanga, an yi nasarar ceto wadanda harin ya rutsa da su.

Daraktan, ya yaba da irin namijin kokarin da sojojin ke yi, yayin da ya kuma jaddada kudirin gwamnatin Gwamna Nasir Idris na tallafa wa hukumomin tsaro a jihar don tabbatar cewa tsaro ya inganta, Inji shi.

Ya ce baya ga ci gaba da tallafin kayan aiki da gwamna ke baiwa jami’an tsaro, ya kara da cewa ” matsayin Gwamnan jihar babban jami’in tsaro na jihar ya ba da umarnin yin ga duk jami’an tsaro da su magance duk wata barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar. Inji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.