• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun Bataliya ta daya Barikin Dukku da hadin guiwar ‘Yan banga a jihar kebbi sun yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su tare da fatattakar ‘yan bindiga da dama a dajin karamar hukumar Shanga da ke Jihar Kebbi.

Nasarar da aka samu ta biyo bayan wani aikin ceto da rundunar hadin guiwa da jami’an tsaro suka yi a dajin karamar hukumar Shanga bayan rahoton wadanda aka yi garkuwa da su.

  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Tare Da Gano Bindigar AK47 A Kebbi
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A cewar daraktan tsaro, AbdulRahman Usman, maza shidan da aka ceto duk sun kasance cikin koshin lafiya da kuma walwala da jin dadi kuma mayar da su cikin iyalansu.

Ya bayyana cewa dakarun Bataliya ta 1 na Dukku Barrack da ke Birinin Kebbi da ke aikin share fage tare da hadin gwiwar ‘yan banga na yankin sun kai wani samame a tsaunin Kogon Damisa da ke kusa da Saminaka a karamar hukumar Shanga, wani gari mai iyaka tsakanin Kebbi da Jihar Neja.

A cewarsa, a yayin samamen, rundunar ta fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su.

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

“An ba da rahoton bacewar wadanda aka ceto, an yi garkuwa da su na dan wani lokaci, kafin samun nasarar ceto su.

An sanar da jami’an tsaro a yankin da suka hada da sojoji da ‘yan banga inda suka shiga cikin dajin Shanga, an yi nasarar ceto wadanda harin ya rutsa da su.

Daraktan, ya yaba da irin namijin kokarin da sojojin ke yi, yayin da ya kuma jaddada kudirin gwamnatin Gwamna Nasir Idris na tallafa wa hukumomin tsaro a jihar don tabbatar cewa tsaro ya inganta, Inji shi.

Ya ce baya ga ci gaba da tallafin kayan aiki da gwamna ke baiwa jami’an tsaro, ya kara da cewa ” matsayin Gwamnan jihar babban jami’in tsaro na jihar ya ba da umarnin yin ga duk jami’an tsaro da su magance duk wata barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar. Inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan BangaJami'an TsaroJihar Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Ya Biya Tarar Naira Miliyan 585 Domin A Saki Daurarru 4,068

Next Post

Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

Related

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

34 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 hour ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

17 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

19 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

1 day ago
Next Post
Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

Ko Zai Yiwu A Kori Manchester City Da Liverpool Daga Gasar Firimiya?

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.