• English
  • Business News
Friday, June 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

by Abubakar Sulaiman
22 hours ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojojin Nijeriya ɓangaren Operation Fasar Yamma ta samu nasarar hallaka fitaccen ƙasurgumin ɗan ta’adda mai suna Auta tare da wasu mutane 13 a jihar Zamfara, kamar yadda shalƙwatar Tsaron Nijeriya ta bayyana.

Daraktan hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojoji, Manjo Janar Markus Kangye, ya ce dakarun Mobile Strike Team (MST) sun gudanar da wani samame mai ƙarfi a ranar 10 ga Yuni, 2025, a yankin Ƙunchin Kalgo da ke ƙaramar hukumar Tsafe, inda suka hallaka waɗannan ‘yan ta’adda.

  • Sojoji Sun Kashe Babban Kwamandan Boko Haram A Jihar Yobe
  • Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Manjo Janar Kangye ya ce Auta da abokansa — Abdul Jamilu da Salisu — na daga cikin waɗanda aka kashe a wannan hari, kuma ana danganta su da aikata munanan laifuka da tashe-tashen hankula a yankin.

Har ila yau, bayanan sirri sun nuna cewa wasu shugabannin ‘yan ta’adda biyu, ciki har da wanda aka fi sani da Babayé, an kashe su a wannan farmaki. A wani samame daban, Sale Ado Madele (wanda ake kira Sarki), babban ɗan sanannen shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru, shi ma ya rasa ransa.

Sojoji

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Baya ga haka, Sojojin sun kashe ƙarin ‘yan ta’adda goma da suka taru kusa da wani gidan mai a Danjibga, waɗanda ake zargin sun kasance cikin wata tawagar da Dogo Sule ya tara domin kitsa hari. Manjo Janar Kangye ya jaddada cewa rundunar Soji za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaSojojiƳan ta'adda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

Next Post

Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

Related

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

1 hour ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

3 hours ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

5 hours ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

20 hours ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

1 day ago
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

1 day ago
Next Post
Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

June 13, 2025
gombe

Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran

June 13, 2025
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

June 13, 2025
Sojoji

Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya

June 13, 2025
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

June 13, 2025
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

June 13, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

June 13, 2025
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

June 13, 2025
nijeriya

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

June 13, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.