• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
Sojoji

Sojojin rundunar 12 na rundunar Sojin Nijeriya sun kashe wani shahararren shugaban ƴan bindiga, Kachalla Balla, tare da wasu mabiyansa guda biyar a lokacin wani samame da ake ci gaba da gudanarwa a jihar Kogi.

Jami’in hulɗa da jama’a na bataliya ta 12, Laftanar Hassan Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Lokoja ranar Lahadi. Ya ce an kashe Kachalla Balla ne a ranar 5 ga Satumba, yayin musayar wuta da Sojojin suka yi da ƴan bindigar a mafakar su da ke kusa da Tunga, a ƙarƙashin aikin Operation EGWUA A TITE II.

  • Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
  • Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Abdullahi ya bayyana cewa Sojojin, tare da haɗin gwuiwar rundunar haɗaka (OHF), sun yi kwanton ɓauna a kan hanyar da ake zargin ƴan bindiga ke bi don samun kayan agaji a gadar Agbede–Adankoo (Mosalanci Boka). A wurin, an kashe wani ɗan leƙen asirinsu, tare da kwace babur, da wayoyi biyu, da sinƙin harsashin bindiga AK-47 mai ɗauke da harsasai 20.

A wani sumame makamancin haka, sojojin Bataliya ta 126 sun yi artabu da ƴan bindiga a cikin garin Tunga, inda suka kashe biyu daga cikinsu. Daga bisani, kwamandan, Birgediya Janar Kasim Umar Sidi, ya jagoranci wani farmaki, inda aka lalata sansanonin ƴan bindiga da dama.

Haka kuma, a ranar 2 ga Satumba, da taimakon jiragen yaƙi na 405, an kai hari kan ƴan bindiga a Ankomi, inda aka kashe da dama daga cikinsu. A tsakanin 3 zuwa 4 ga Satumba kuma, Sojoji sun yi bincike a Aleke, Ungwan Soni da Ungwan Nyaba, inda suka ceto wani mai suna Pabo Suleiman tare da ƴaƴansa biyu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Abdullahi ya tabbatar da cewa rundunar Sojin Nijeriya za ta ci gaba da aiyukanta don kawar da ƴan bindiga da sauran barazanar tsaro a jihar Kogi da kewaye.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

October 26, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.