• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kawar da wasu jiga-jigan ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo, Halilu Buzu, a Jihar Zamfara da Alhaji Ganai da abokinsa Yellow Kano a Jihar Kaduna. 

A cewar majiyae sojin, an kashe ‘yan ta’addan da mayakan ne a wasu hare-hare ta sama guda biyu biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu.

  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD
  • 2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

An kashe Halilu Buzu ne a ranar 21 ga watan Oktoba, 2022 a yayin wani harin da aka kai musu ta sama a sansaninsu da ke karamar hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.

Wani babban jami’i ya ce an ba da izinin kai harin ta sama ne bayan wasu bayanan sirri da aka samu sun nuna cewa wani kasurgumin dan ta’adda mai suna Halilu Buzu da ke garin Sububu a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ya shirya ganawa da wasu daga cikin sojojin da ke yankin.

Hukumar leken asirin ta kuma bayyana inda da kuma ainihin wurin da yake ajiye kayan aikinsa inda shi da tawagarsa suka saba ajiye harsashi da ababen hawa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“Saboda haka, jiragen yaki NAF sun kai farmaki a lokaci guda inda taron ya gudana da kuma cibiyar hada kayan aiki.

“An hangi wata wuta ta tashi bayan kai harin, lamarin da ke nuni da cewa akwai yuwuwar wurin ya kunshi wani abu mai zafi,” in ji jami’in.

Majiyar ta ce binciken da aka yi a kan barnar shanu ya nuna wurin da taron ya gudana da kuma wurin da aka a lalata.

Ya ce bayanan da aka samu a baya-bayan nan sun nuna cewa lallai an kawar da Halilu Buzu a harin da aka kai ta sama tare da wasu shugabannin ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa, “Kawar da Halilu Buzu ya zo ne a matsayin abun farin ciki ga mazauna yankin Sububu, Anka (Bayan Daji) da kuma mahadar Bayan Ruwa a Jihar Zamfara bisa la’akari da kwarewarsa wajen ta’addanci da azabtar da wadanda yake yin garkuwa da su, tuni rashinsa ya rage yawaitar faruwar kai hare-hare da garkuwa da mutane, satar shanu da sauran ayyukan ta’addanci a yankin.”

Ya ce an kai irin wannan harin ta sama a ranar 14 ga watan Nuwamba, 2022 a wani wurin da wani kasurgumin dan ta’adda yake a unguwar Alhaji Ganai a dajin Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Ya ce harin ta sama ya zama wajibi ne bayan da hukumar leken asiri ta sa ido da bin diddigi, da kuma gano yadda al’amuran Alhaji Ganai da dakarunsa ke a wurin.

“Bayanan sirri sun nuna cewa an lalata wasu gine-ginen da ke wurin da suka hada da gidan Alhaji Ganai da babura, sannan an kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da Yello Kano, na hannun damar shugaban ‘yan ta’adda, Musa Balejo da wasu kasurguman ‘yan ta’adda bakwai bayan harin,” a cewarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaKadunaKasurgumin Dan BindigaShugabannin 'Yan BindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano

Next Post

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

24 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sojoji

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.