• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kawar da wasu jiga-jigan ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo, Halilu Buzu, a Jihar Zamfara da Alhaji Ganai da abokinsa Yellow Kano a Jihar Kaduna. 

A cewar majiyae sojin, an kashe ‘yan ta’addan da mayakan ne a wasu hare-hare ta sama guda biyu biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu.

  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD
  • 2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

An kashe Halilu Buzu ne a ranar 21 ga watan Oktoba, 2022 a yayin wani harin da aka kai musu ta sama a sansaninsu da ke karamar hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.

Wani babban jami’i ya ce an ba da izinin kai harin ta sama ne bayan wasu bayanan sirri da aka samu sun nuna cewa wani kasurgumin dan ta’adda mai suna Halilu Buzu da ke garin Sububu a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ya shirya ganawa da wasu daga cikin sojojin da ke yankin.

Hukumar leken asirin ta kuma bayyana inda da kuma ainihin wurin da yake ajiye kayan aikinsa inda shi da tawagarsa suka saba ajiye harsashi da ababen hawa.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

“Saboda haka, jiragen yaki NAF sun kai farmaki a lokaci guda inda taron ya gudana da kuma cibiyar hada kayan aiki.

“An hangi wata wuta ta tashi bayan kai harin, lamarin da ke nuni da cewa akwai yuwuwar wurin ya kunshi wani abu mai zafi,” in ji jami’in.

Majiyar ta ce binciken da aka yi a kan barnar shanu ya nuna wurin da taron ya gudana da kuma wurin da aka a lalata.

Ya ce bayanan da aka samu a baya-bayan nan sun nuna cewa lallai an kawar da Halilu Buzu a harin da aka kai ta sama tare da wasu shugabannin ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa, “Kawar da Halilu Buzu ya zo ne a matsayin abun farin ciki ga mazauna yankin Sububu, Anka (Bayan Daji) da kuma mahadar Bayan Ruwa a Jihar Zamfara bisa la’akari da kwarewarsa wajen ta’addanci da azabtar da wadanda yake yin garkuwa da su, tuni rashinsa ya rage yawaitar faruwar kai hare-hare da garkuwa da mutane, satar shanu da sauran ayyukan ta’addanci a yankin.”

Ya ce an kai irin wannan harin ta sama a ranar 14 ga watan Nuwamba, 2022 a wani wurin da wani kasurgumin dan ta’adda yake a unguwar Alhaji Ganai a dajin Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Ya ce harin ta sama ya zama wajibi ne bayan da hukumar leken asiri ta sa ido da bin diddigi, da kuma gano yadda al’amuran Alhaji Ganai da dakarunsa ke a wurin.

“Bayanan sirri sun nuna cewa an lalata wasu gine-ginen da ke wurin da suka hada da gidan Alhaji Ganai da babura, sannan an kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da Yello Kano, na hannun damar shugaban ‘yan ta’adda, Musa Balejo da wasu kasurguman ‘yan ta’adda bakwai bayan harin,” a cewarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaKadunaKasurgumin Dan BindigaShugabannin 'Yan BindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano

Next Post

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

7 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

12 hours ago
Next Post
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.