• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kawar da wasu jiga-jigan ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo, Halilu Buzu, a Jihar Zamfara da Alhaji Ganai da abokinsa Yellow Kano a Jihar Kaduna. 

A cewar majiyae sojin, an kashe ‘yan ta’addan da mayakan ne a wasu hare-hare ta sama guda biyu biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu.

  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD
  • 2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

An kashe Halilu Buzu ne a ranar 21 ga watan Oktoba, 2022 a yayin wani harin da aka kai musu ta sama a sansaninsu da ke karamar hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.

Wani babban jami’i ya ce an ba da izinin kai harin ta sama ne bayan wasu bayanan sirri da aka samu sun nuna cewa wani kasurgumin dan ta’adda mai suna Halilu Buzu da ke garin Sububu a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ya shirya ganawa da wasu daga cikin sojojin da ke yankin.

Hukumar leken asirin ta kuma bayyana inda da kuma ainihin wurin da yake ajiye kayan aikinsa inda shi da tawagarsa suka saba ajiye harsashi da ababen hawa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

“Saboda haka, jiragen yaki NAF sun kai farmaki a lokaci guda inda taron ya gudana da kuma cibiyar hada kayan aiki.

“An hangi wata wuta ta tashi bayan kai harin, lamarin da ke nuni da cewa akwai yuwuwar wurin ya kunshi wani abu mai zafi,” in ji jami’in.

Majiyar ta ce binciken da aka yi a kan barnar shanu ya nuna wurin da taron ya gudana da kuma wurin da aka a lalata.

Ya ce bayanan da aka samu a baya-bayan nan sun nuna cewa lallai an kawar da Halilu Buzu a harin da aka kai ta sama tare da wasu shugabannin ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa, “Kawar da Halilu Buzu ya zo ne a matsayin abun farin ciki ga mazauna yankin Sububu, Anka (Bayan Daji) da kuma mahadar Bayan Ruwa a Jihar Zamfara bisa la’akari da kwarewarsa wajen ta’addanci da azabtar da wadanda yake yin garkuwa da su, tuni rashinsa ya rage yawaitar faruwar kai hare-hare da garkuwa da mutane, satar shanu da sauran ayyukan ta’addanci a yankin.”

Ya ce an kai irin wannan harin ta sama a ranar 14 ga watan Nuwamba, 2022 a wani wurin da wani kasurgumin dan ta’adda yake a unguwar Alhaji Ganai a dajin Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Ya ce harin ta sama ya zama wajibi ne bayan da hukumar leken asiri ta sa ido da bin diddigi, da kuma gano yadda al’amuran Alhaji Ganai da dakarunsa ke a wurin.

“Bayanan sirri sun nuna cewa an lalata wasu gine-ginen da ke wurin da suka hada da gidan Alhaji Ganai da babura, sannan an kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da Yello Kano, na hannun damar shugaban ‘yan ta’adda, Musa Balejo da wasu kasurguman ‘yan ta’adda bakwai bayan harin,” a cewarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaKadunaKasurgumin Dan BindigaShugabannin 'Yan BindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano

Next Post

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Related

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

7 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

9 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

13 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

14 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

19 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 day ago
Next Post
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.