ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

by Buhari Abba Rano
4 years ago
Kano

Yayin da ake kara kusantar zabe a Nijeriya, jam’iyyun siyasa da wadanda su ka fito takara a mukamai na ci gaba da yada manufa tare da bayyana irin kyawawan manufofin da suke burin aiwatarwa, idan sun kai ga nasara a zaben shekarar 2023 da ke tafe.

A Jihar Kano, da ta zama cibiyar siyasar Nijeriya, akwai masu neman kujerar gwamna a jam’iyyu daban-daban kuma ake jin duriyarsu da kuma bayyana wa Kanawan irin tanadin da suka yi musu idan su ka kai ga nasara.

  • Gobara Ta Kone Shaguna 15 Da Lalata Kaya Na Miliyan 19 A Jihar Kwara
  • Gobara Ta Yi Barna A Kasuwar Sayar Da Kayan Masarufi Ta Singa Da Ke Kano.

Jami’yyar APC ce ke mulkin Jihar Kano, inda suke da Dakta Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin dan takara, sai kuma jami’yyar NNPP ta tsohon gwamna Rabi’u Kwankwaso da suke da Abba Kabiru Yusuf da kuma jami’yyar PDP da suke da Sadiq Aminu Bashir Wali a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar takara a 2023.

ADVERTISEMENT

Wali, wanda tsohon Kwamishinan albarkatun ruwa ne a gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, ya zama dan takarar gwamnan ne a jam’iyyar PDP bayan da ya yi nasara a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.

Tun da farko jam’iyyar PDP a Kano ta fuskantar rikici a kan wane ne halastaccen dan takarar gwamnan a jami’yyar.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Muhammad Abacha da Sadiq Aminu Wali kowane a cikinsu na jin shi ne halastaccen dan takarar jam’iyyar, biyo bayan rikicin zaben fidda gwani da kowanne bangare ya gudanar karkashin sa idon hukumar zabe ta kasa INEC.

Shugabancin jam’iyya bangaren Shehu Wada Sagagi, ya gabatar da zaben fidda gwani na jam’iyyar kuma a matsayarsa, Muhammed Abacha ne ya samu nasara.

Bayan zuwa kotu da aka yi, kotu ta sake ayyana Sadiq Wali a matsayin halastaccen dan takarar da zai yi wa PDP takarar gwamna a Kano.

Sai dai duk da wannan damar da Wali din ya samu amma har yanzu ya gaza fitowa fili ya bayyana wa Kanawa manufofinsa da kuma irin tanadin da gwamnatinsu ta yi musu idan ya kai ga nasara.

Haka kuma wani abin mamaki ga lamarin Sadiq Aminu Wali, shi ne yadda ya ke biris da gayyatar da manyan kungiyoyi ke shirya wa ‘yan takarar gwamna a Kano, inda al’umma suke kallon ko bai shiryawa takarar ba.

Haka zalika, ko a lokacin da Sadiq Wali din ya ke Kwamishinan ruwa na Kano, babu wani abin a zo a gani da ya tabuka domin sai da ta kai ga yara ‘yan makaranta ba sa samun zuwa makaranta ko kuma ba sa zuwa da wuri sakamakon fadi-tashin neman ruwa.

Masu sharhi a kan al’amuran siyasar Kano da sauran ‘yan siyasar jihar, sun dade da bayyana Sadiq Aminu Wali, a matsayin dan gatan da bai san wanne hali talaka a Jihar Kano ke ciki ba, kuma ba shi da wani kuduri ko manufa da zai ciyar da Kano gaba idan ya zama gwamna a 2023.

Mafi yawan al’ummar Jihar Kano na kallon Sadiq Aminu Wali a matsayin “Sabon Yankan Rake” a siyasa domin ba shi da wata kwarewa ko gogewar da zai ja ragamar shugabancin Jihar Kano da ke da sama da mutum miliyan tara.

Kuma shi ma ya tabbatar wa da duniya hakan la’akari da yadda ya gaza fitowa fili ya tallata takararsa da manufofinsa ga Kanawa.

Babu shakka ya zama wajibi ga al’ummar Jihar Kano da su zabi jajirtaccen mutumin da ya ke da ilimin addinin Islama da kuma na zamani tare da gogewar aiki da kuma manufa wanda ya ke da sanayya tsakanin manyan ‘yan kasuwa da ‘yan boko da ma’aikatan gwamnati da kuma goyon bayan kungiyoyin fararen hula, ba wai su bi rububi wajen zabar “Yankan Rake” ko dan gatan da bai san daga ina zai fara magance matsalolin da su ka yi wa jihar katutu ba.

Buhari Abba dan jarida ne ya rubuto daga Kano, Najeriya

[email protected]

Kano
Buhari Abba Rano
+ postsBio
  • Buhari Abba Rano
    https://hausa.leadership.ng/author/buhari-abba-rano/
    Ficewar Malam Shekarau Daga NNPP: Me Ya Sa Hankalin ‘Yan Kwankwasiyya Ya Tashi?
  • Buhari Abba Rano
    https://hausa.leadership.ng/author/buhari-abba-rano/
    Yaro Tsaya Matsayinka: Ina Makomar Sha’aban Sharada A Siyasar Kano?

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Jihar Bayelsa Kalubale Ne Mai Girman Gaske – Majalisar Dinkin Duniya

Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.