• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama, Sun Kwato Makamai A Zamfara

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Rundunar Sojojin Saman Nijeriya ke kara kai hare-hare a yankunan ‘yan ta’adda, dakarun rundunar Birget ta 1, Rundunar hadin gwiwa ta Arewa maso Yamma, tare da Operation Fansan Yamma sun kashe ‘yan ta’adda da dama ciki har da wani dan ta’adda mai suna Sani Rusu tare da kwato makamai a jihar Zamfara.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘Operation Fansan Yamma’, Laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, ya rabawa manema labarai a Gusau ranar Litinin.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kashe ‘Yan Bindiga 80 A Katsina
  • Na Ɗauki Rarara Tamkar Mahaifi A Wajena – Tijjani Asase

Sanarwar ta ce, sojojin sun kai samame ne a kauyen Bamamu da ke karamar hukumar Tsafe a ranar Asabar 4 ga watan Janairu, 2025 inda suka yi taho mu gamu da ‘yan ta’addan.

 

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

A arangamar, Sojojin sun yi nasarar kawar da wani fitaccen dan bindiga, tarwatsa matsugunansu tare da kwato tarin makamai.

 

Hakazalika, sanarwar ta kara da cewa, a wani samame na daban, rundunar sojin sama ta Operation Fansan Yamma ta kai farmaki ta sama kan ‘yan ta’addan da suka hadu a tsakanin Fakai da Kware a karamar hukumar Shinkafi a ranar 30 ga watan Disamba 2024.

 

“An kaddamar da wannan harin ta sama ne a matsayin martani ga bayanan sirri da ke nuni da cewa ‘yan ta’adda a karkashin jagorancin Bello Turji sun gudanar da taro a yankin.

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Sojojin sun kuma kai farmaki kan sansanin Bello Turji da ke yankin Chida a Shinkafi a ranar 5 ga watan Janairun 2025. Binciken jirgin yakin ya nuna cewa, an yi wa ‘yan ta’addan mummunar barna a wadannan hare-hare tare da jikkata ‘yan ta’adda da dama inda aka tarwatsa maboyarsu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kashe ‘Yan Bindiga 80 A Katsina

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Satar Mota A Kano

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

6 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

8 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

10 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

12 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

15 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Satar Mota A Kano

'Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Satar Mota A Kano

LABARAI MASU NASABA

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

July 30, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.