• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

An kashe mahara da dama

by Muhammad
3 years ago

Dakarun Operation Hadin Kai da ke yankin Arewa maso Gabas, sun kashe ‘yan ta’addar Boko Haram da ba a tantance adadinsu ba, tare da kubutar da wata ‘yar makarantar Chibok, wadda ta haifi tagwaye a lokacin da aka yi garkuwa da su.

Sojojin tare da hadin guiwar CJTF sun cimma wannan nasara ne a ranar 29 ga Satumba, 2022 bayan da suka kai farmaki a yankin Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād.

  • 2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027
  • An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

Wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, kuma ya samu ga wakilinmu, ya nuna cewa sojojin sun yi artabu da ‘yan ta’addar, inda suka yi nasarar kawar da dama daga cikinsu a cikin lamarin, yayin da kuma aka yi nasarar dakile su. wasu da dama sun tsere da munanan raunukan harbin bindiga.

“A yayin arangamar, sojoji sun yi nasarar ceto Yana Pogu, ‘yar Chibok, wacce ke lamba 19 a jerin ‘yan matan da suka bata tare da ‘ya’yanta hudu.

“An same ta da wasu tagwaye ‘yan watanni hudu a cikin wani yanayi mara kyau.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

“Wasu daga cikin ‘yan ta’addar da suka tsere sun yi yunkurin yi wa sojoji kwanton bauna amma yayin da suke aiki da bayanan sirri, sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa.

“An ceto karin mata bayan haduwarsu. An mayar da su runduna ta 21 Bama, domin kula da lafiyarsu,” inji majiyar.

Wakilinmu ya tuna cewa a watan Afrilun 2014 ne ‘yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa da dalibai mata 276 yawancinsu Kiristoci ‘yan tsakanin shekaru 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ‘yan mata ta gwamnati da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno.

Ya zuwa yanzu kusan 100 daga cikin ‘yan matan na nan a yankunan ‘yan ta’addar, yayin da wadanda suka yi sa’a ko dai sojoji ne suka kubutar da su ko kuma sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

katsina
Labarai

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.