• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

An kashe mahara da dama

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun Operation Hadin Kai da ke yankin Arewa maso Gabas, sun kashe ‘yan ta’addar Boko Haram da ba a tantance adadinsu ba, tare da kubutar da wata ‘yar makarantar Chibok, wadda ta haifi tagwaye a lokacin da aka yi garkuwa da su.

Sojojin tare da hadin guiwar CJTF sun cimma wannan nasara ne a ranar 29 ga Satumba, 2022 bayan da suka kai farmaki a yankin Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād.

  • 2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027
  • An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

Wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, kuma ya samu ga wakilinmu, ya nuna cewa sojojin sun yi artabu da ‘yan ta’addar, inda suka yi nasarar kawar da dama daga cikinsu a cikin lamarin, yayin da kuma aka yi nasarar dakile su. wasu da dama sun tsere da munanan raunukan harbin bindiga.

“A yayin arangamar, sojoji sun yi nasarar ceto Yana Pogu, ‘yar Chibok, wacce ke lamba 19 a jerin ‘yan matan da suka bata tare da ‘ya’yanta hudu.

“An same ta da wasu tagwaye ‘yan watanni hudu a cikin wani yanayi mara kyau.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Wasu daga cikin ‘yan ta’addar da suka tsere sun yi yunkurin yi wa sojoji kwanton bauna amma yayin da suke aiki da bayanan sirri, sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa.

“An ceto karin mata bayan haduwarsu. An mayar da su runduna ta 21 Bama, domin kula da lafiyarsu,” inji majiyar.

Wakilinmu ya tuna cewa a watan Afrilun 2014 ne ‘yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa da dalibai mata 276 yawancinsu Kiristoci ‘yan tsakanin shekaru 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ‘yan mata ta gwamnati da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno.

Ya zuwa yanzu kusan 100 daga cikin ‘yan matan na nan a yankunan ‘yan ta’addar, yayin da wadanda suka yi sa’a ko dai sojoji ne suka kubutar da su ko kuma sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Next Post

Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

40 minutes ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

2 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

3 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

7 hours ago
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

9 hours ago
Next Post
Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.