ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

An kashe mahara da dama

by Muhammad
4 years ago

Dakarun Operation Hadin Kai da ke yankin Arewa maso Gabas, sun kashe ‘yan ta’addar Boko Haram da ba a tantance adadinsu ba, tare da kubutar da wata ‘yar makarantar Chibok, wadda ta haifi tagwaye a lokacin da aka yi garkuwa da su.

Sojojin tare da hadin guiwar CJTF sun cimma wannan nasara ne a ranar 29 ga Satumba, 2022 bayan da suka kai farmaki a yankin Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād.

  • 2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027
  • An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

Wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, kuma ya samu ga wakilinmu, ya nuna cewa sojojin sun yi artabu da ‘yan ta’addar, inda suka yi nasarar kawar da dama daga cikinsu a cikin lamarin, yayin da kuma aka yi nasarar dakile su. wasu da dama sun tsere da munanan raunukan harbin bindiga.

ADVERTISEMENT

“A yayin arangamar, sojoji sun yi nasarar ceto Yana Pogu, ‘yar Chibok, wacce ke lamba 19 a jerin ‘yan matan da suka bata tare da ‘ya’yanta hudu.

“An same ta da wasu tagwaye ‘yan watanni hudu a cikin wani yanayi mara kyau.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

“Wasu daga cikin ‘yan ta’addar da suka tsere sun yi yunkurin yi wa sojoji kwanton bauna amma yayin da suke aiki da bayanan sirri, sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa.

“An ceto karin mata bayan haduwarsu. An mayar da su runduna ta 21 Bama, domin kula da lafiyarsu,” inji majiyar.

Wakilinmu ya tuna cewa a watan Afrilun 2014 ne ‘yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa da dalibai mata 276 yawancinsu Kiristoci ‘yan tsakanin shekaru 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ‘yan mata ta gwamnati da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno.

Ya zuwa yanzu kusan 100 daga cikin ‘yan matan na nan a yankunan ‘yan ta’addar, yayin da wadanda suka yi sa’a ko dai sojoji ne suka kubutar da su ko kuma sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

Sirrin Tsaftace Hakora Su Koma Farare Sal (3)

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.