• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

bySadiq
2 years ago
Nijar

Sojojin da ke mulkin Nijar na ci gaba da neman goyon bayan kasashe musamman wadanda ba su nuna adawa da juyin mulkin da suka yi ba a kasar ba.

A ranar Talata firaministan Nijar da sojoji suka nada, Ali Mahaman Lamine Zeine, tare da wasu mambobin majalisar mulkin soja biyu suka ziyarci Chadi domin tattaunawa da shugaban kasar, Janar Mahamat Idriss Deby.

  • Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye
  • Manchester City Ta Lashe Kofin Super Cup Bayan Lallasa Sevilla

Zeine, wanda ya je a matsayin fuskar diflomasiyya ta gwamnatin soja – ya ce a yanzu kasarsa na karkashin gwamnatin mulkin soji, yana mai cewa a shirye suke da su bude kofar tattaunawa.

Kazalika, sojojin mulkin sun tura wata tawaga zuwa Guinea ranar Asabar da ta gabata, duka dai da zimmar neman goyon baya.

Kafin haka, sabon ministan tsaron Nijar, Janar Salifou Mody, ya je Mali a ranar Juma’a cikin wata gajeriyar ziyara.

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Ƙasashen Mali da Burkina Faso da Gueinea mambobin ECOWAS ne – kungiyar da ke raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma – amma ta dakatar da su sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a kasashen.

Haka nan dukkansu sun ci alwashin goya wa Nijar baya idan dakarun ECOWAS ko na wata kasar waje suka kai wa sojojin hari.

A karshen makon da ya gabata gwamnatin sojin Mali ta sanar cewa za ta aika wa Nijar nau’in kayan abinci na hatsi kamar dawa masara da gero saboda takunkumin ECOWAS da ya hana sayar mata da kayayyaki.

Chadi ba ta cikin kungiyar ECOWAS, sannan kuma ba ta nuna adawa karara da juyin mulkin da sojojin Nijar suka yi ba, amma ta bayyana a fili cewa ba za ta goyi bayan yin amfani da karfi a kan makwabciyar tata ba.

Har yanzu ECOWAS na ci gaba da yunkurin difilomasiyya don sasanta rikicin siyasar, duk da barazanar amfani da karfin soja don taka wa sojojin karkashin Janar Abdourahmane Tchiani birki.

A ranar Alhamis da Juma’a hafsoshin tsaron kungiyar za su yi taro a birnin Accra na Ghana don ci gaba da tattaunawa bayan shugabannin Ecowas din sun ba su umarnin ɗaura damarar kutsawa Nijar a makon da ya gabata.

A gefe guda kuma, fitattun mutane da kungiyoyi a Nijeriya na ci gaba da nuna adawa da yin amfani da karfin yayin da Shugaba Bola Tinubu, a matsayinsa na shugaban ECOWAS, yake jagorantar yunkurin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
Emefiele Ya Maka DSS A Kotu Kan Tsare Shi

An Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Tuhume-Tuhume 20

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version