• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

by Sadiq
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Gwamnatin Sojin Nijar Ta Yi Sabbin Nade-Nade
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojojin da ke mulkin Nijar na ci gaba da neman goyon bayan kasashe musamman wadanda ba su nuna adawa da juyin mulkin da suka yi ba a kasar ba.

A ranar Talata firaministan Nijar da sojoji suka nada, Ali Mahaman Lamine Zeine, tare da wasu mambobin majalisar mulkin soja biyu suka ziyarci Chadi domin tattaunawa da shugaban kasar, Janar Mahamat Idriss Deby.

  • Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye
  • Manchester City Ta Lashe Kofin Super Cup Bayan Lallasa Sevilla

Zeine, wanda ya je a matsayin fuskar diflomasiyya ta gwamnatin soja – ya ce a yanzu kasarsa na karkashin gwamnatin mulkin soji, yana mai cewa a shirye suke da su bude kofar tattaunawa.

Kazalika, sojojin mulkin sun tura wata tawaga zuwa Guinea ranar Asabar da ta gabata, duka dai da zimmar neman goyon baya.

Kafin haka, sabon ministan tsaron Nijar, Janar Salifou Mody, ya je Mali a ranar Juma’a cikin wata gajeriyar ziyara.

Labarai Masu Nasaba

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

Ƙasashen Mali da Burkina Faso da Gueinea mambobin ECOWAS ne – kungiyar da ke raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma – amma ta dakatar da su sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a kasashen.

Haka nan dukkansu sun ci alwashin goya wa Nijar baya idan dakarun ECOWAS ko na wata kasar waje suka kai wa sojojin hari.

A karshen makon da ya gabata gwamnatin sojin Mali ta sanar cewa za ta aika wa Nijar nau’in kayan abinci na hatsi kamar dawa masara da gero saboda takunkumin ECOWAS da ya hana sayar mata da kayayyaki.

Chadi ba ta cikin kungiyar ECOWAS, sannan kuma ba ta nuna adawa karara da juyin mulkin da sojojin Nijar suka yi ba, amma ta bayyana a fili cewa ba za ta goyi bayan yin amfani da karfi a kan makwabciyar tata ba.

Har yanzu ECOWAS na ci gaba da yunkurin difilomasiyya don sasanta rikicin siyasar, duk da barazanar amfani da karfin soja don taka wa sojojin karkashin Janar Abdourahmane Tchiani birki.

A ranar Alhamis da Juma’a hafsoshin tsaron kungiyar za su yi taro a birnin Accra na Ghana don ci gaba da tattaunawa bayan shugabannin Ecowas din sun ba su umarnin É—aura damarar kutsawa Nijar a makon da ya gabata.

A gefe guda kuma, fitattun mutane da kungiyoyi a Nijeriya na ci gaba da nuna adawa da yin amfani da karfin yayin da Shugaba Bola Tinubu, a matsayinsa na shugaban ECOWAS, yake jagorantar yunkurin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumECOWASJuyin MulkiNijarSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye

Next Post

An Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Tuhume-Tuhume 20

Related

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

6 days ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

1 week ago
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

2 weeks ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

2 weeks ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

2 weeks ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

2 weeks ago
Next Post
Emefiele Ya Maka DSS A Kotu Kan Tsare Shi

An Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Tuhume-Tuhume 20

LABARAI MASU NASABA

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.