• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 44, Sun Damke 50 Cikin Mako 2 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 44, Sun Damke 50 Cikin Mako 2 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar tsaro ta kasa ta ce dakarun Hadin Kai da Hadarin Daji sun kashe ‘yan ta’adda akalla 44 tare da kama sama da 50 a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma a cikin mako biyu da suka gabata. 

Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro Musa Danmadami ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da suka saba yi duk mako biyu kan ayyukan rundunar, ranar Alhamis a Abuja.

  • Da Dumi-Dumi: An Harbi Tsohon Firaministan Pakistan, Imran Khan 
  • Kammala aikin tashar ruwa mai zurfi ta Lagos zai ingiza bunkasar tattalin arzikin Najeriya

A yankin Arewa maso Gabas, Mista Danmadami ya ce a tsakanin ranar 20 ga watan Oktoba zuwa ranar 2 ga watan Nuwamba, sojojin Operation Hadin Kai sun kama wasu mutane 27 da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram ne da kuma mayakan ISWAP tare da kashe 19.

Mista Danmadami ya kara da cewa sojojin sun kwato manyan makamai da alburusai na nau’o’i daban-daban da kuma sauran kayan aiki a lokacin.

A cewarsa, a ranar 21 ga watan Oktoban da ya gabata ne, rundunar ta kai farmaki ta sama a kan ayarin motocin ‘yan ta’addan akan hanyar Tunbum Aliyu, kusa da tafkin Chadi, wurin da ‘yan ta’addan ke kudu maso yammacin Maiduguri.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Ya ce hare-haren sun kawar da ‘yan ta’adda da dama da kuma manyan motocin bindigu guda bakwai da sauran makamai.

“Hakazalika, bisa sahihin bayanan sirri na ‘yan ta’addan da ke yin sintiri a cikin unguwannin Abulum da Njibul da ke kusa da dajin Sambisa, rundunar ta kai farmaki a wuraren a lokaci daya tare da kawar da dimbin ‘yan ta’addan, yayin da aka ga wadanda suka samu raunuka sun yi kaca-kaca wasu kuma sun tsere.

“Hakazalika, sojojin tare da hadin gwiwar jami’an sa-kai a ranar 22 ga watan Oktoba, sun kama wani mutum da ake zargi da mallakar katin zabe guda 67 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke garin Shuwari a karamar hukumar Maiduguri ta Jihar Borno.

“Haka kuma, a wannan sansani, an kashe wani sanannen dan ta’adda, Lawan Yashin, wanda ya yi yunkurin tserewa da ganin sojoji.

“A lokacin guda ‘yan ta’addar Boko Haram 145 da iyalansu da suka hada da manya maza 30, manya mata 33 da kananan yara 82 ne suka mika wuya ga sojoji a wurare daban-daban ga sojoji a Arewa maso Gabas,” in ji Danmadami.

A yankin Arewa maso Yamma, kakakin rundunar tsaron, ya ce dakarun hadin gwiwa na Hadarin Daji da Whirl Punch sun kashe ‘yan ta’adda 25, sun kama 18 tare da kubutar da fararen hula 19 a hare-hare daban-daban.

Mista Danmadami, ya ce sojojin sun kuma kwato manyan makamai da alburusai daban-daban da kuma shanu 441 da aka sace.

Ya kara da cewa sojojin a ranar 24 ga watan Oktoba, sun kai wa ‘yan ta’addan hari a kan hanyar Buruku-Angwan Yako-Udawa a karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka ceto fararen hula 10 tare da kwato motoci uku.

Kakakin rundunar, ya ce sojojin sun kuma kashe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wasu mutane tara da aka yi garkuwa da su a Faskari a Jihar Katsina da kuma Anka a Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBornoKadunaKatsinaKisaMakamaiSojojiYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Rangadin Nuna Kashi Na Uku Na Fina-Finan Kasar Sin A Afirka

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

11 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

17 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

21 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

2 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.