• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 44, Sun Damke 50 Cikin Mako 2 

by Sadiq
3 years ago
Sojojin Nijeriya

Hedikwatar tsaro ta kasa ta ce dakarun Hadin Kai da Hadarin Daji sun kashe ‘yan ta’adda akalla 44 tare da kama sama da 50 a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma a cikin mako biyu da suka gabata. 

Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro Musa Danmadami ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da suka saba yi duk mako biyu kan ayyukan rundunar, ranar Alhamis a Abuja.

  • Da Dumi-Dumi: An Harbi Tsohon Firaministan Pakistan, Imran Khan 
  • Kammala aikin tashar ruwa mai zurfi ta Lagos zai ingiza bunkasar tattalin arzikin Najeriya

A yankin Arewa maso Gabas, Mista Danmadami ya ce a tsakanin ranar 20 ga watan Oktoba zuwa ranar 2 ga watan Nuwamba, sojojin Operation Hadin Kai sun kama wasu mutane 27 da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram ne da kuma mayakan ISWAP tare da kashe 19.

Mista Danmadami ya kara da cewa sojojin sun kwato manyan makamai da alburusai na nau’o’i daban-daban da kuma sauran kayan aiki a lokacin.

A cewarsa, a ranar 21 ga watan Oktoban da ya gabata ne, rundunar ta kai farmaki ta sama a kan ayarin motocin ‘yan ta’addan akan hanyar Tunbum Aliyu, kusa da tafkin Chadi, wurin da ‘yan ta’addan ke kudu maso yammacin Maiduguri.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Ya ce hare-haren sun kawar da ‘yan ta’adda da dama da kuma manyan motocin bindigu guda bakwai da sauran makamai.

“Hakazalika, bisa sahihin bayanan sirri na ‘yan ta’addan da ke yin sintiri a cikin unguwannin Abulum da Njibul da ke kusa da dajin Sambisa, rundunar ta kai farmaki a wuraren a lokaci daya tare da kawar da dimbin ‘yan ta’addan, yayin da aka ga wadanda suka samu raunuka sun yi kaca-kaca wasu kuma sun tsere.

“Hakazalika, sojojin tare da hadin gwiwar jami’an sa-kai a ranar 22 ga watan Oktoba, sun kama wani mutum da ake zargi da mallakar katin zabe guda 67 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke garin Shuwari a karamar hukumar Maiduguri ta Jihar Borno.

“Haka kuma, a wannan sansani, an kashe wani sanannen dan ta’adda, Lawan Yashin, wanda ya yi yunkurin tserewa da ganin sojoji.

“A lokacin guda ‘yan ta’addar Boko Haram 145 da iyalansu da suka hada da manya maza 30, manya mata 33 da kananan yara 82 ne suka mika wuya ga sojoji a wurare daban-daban ga sojoji a Arewa maso Gabas,” in ji Danmadami.

A yankin Arewa maso Yamma, kakakin rundunar tsaron, ya ce dakarun hadin gwiwa na Hadarin Daji da Whirl Punch sun kashe ‘yan ta’adda 25, sun kama 18 tare da kubutar da fararen hula 19 a hare-hare daban-daban.

Mista Danmadami, ya ce sojojin sun kuma kwato manyan makamai da alburusai daban-daban da kuma shanu 441 da aka sace.

Ya kara da cewa sojojin a ranar 24 ga watan Oktoba, sun kai wa ‘yan ta’addan hari a kan hanyar Buruku-Angwan Yako-Udawa a karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka ceto fararen hula 10 tare da kwato motoci uku.

Kakakin rundunar, ya ce sojojin sun kuma kashe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wasu mutane tara da aka yi garkuwa da su a Faskari a Jihar Katsina da kuma Anka a Zamfara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.