ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 44, Sun Damke 50 Cikin Mako 2 

by Sadiq
4 years ago
Sojojin Nijeriya

Hedikwatar tsaro ta kasa ta ce dakarun Hadin Kai da Hadarin Daji sun kashe ‘yan ta’adda akalla 44 tare da kama sama da 50 a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma a cikin mako biyu da suka gabata. 

Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro Musa Danmadami ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da suka saba yi duk mako biyu kan ayyukan rundunar, ranar Alhamis a Abuja.

  • Da Dumi-Dumi: An Harbi Tsohon Firaministan Pakistan, Imran Khan 
  • Kammala aikin tashar ruwa mai zurfi ta Lagos zai ingiza bunkasar tattalin arzikin Najeriya

A yankin Arewa maso Gabas, Mista Danmadami ya ce a tsakanin ranar 20 ga watan Oktoba zuwa ranar 2 ga watan Nuwamba, sojojin Operation Hadin Kai sun kama wasu mutane 27 da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram ne da kuma mayakan ISWAP tare da kashe 19.

ADVERTISEMENT

Mista Danmadami ya kara da cewa sojojin sun kwato manyan makamai da alburusai na nau’o’i daban-daban da kuma sauran kayan aiki a lokacin.

A cewarsa, a ranar 21 ga watan Oktoban da ya gabata ne, rundunar ta kai farmaki ta sama a kan ayarin motocin ‘yan ta’addan akan hanyar Tunbum Aliyu, kusa da tafkin Chadi, wurin da ‘yan ta’addan ke kudu maso yammacin Maiduguri.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya ce hare-haren sun kawar da ‘yan ta’adda da dama da kuma manyan motocin bindigu guda bakwai da sauran makamai.

“Hakazalika, bisa sahihin bayanan sirri na ‘yan ta’addan da ke yin sintiri a cikin unguwannin Abulum da Njibul da ke kusa da dajin Sambisa, rundunar ta kai farmaki a wuraren a lokaci daya tare da kawar da dimbin ‘yan ta’addan, yayin da aka ga wadanda suka samu raunuka sun yi kaca-kaca wasu kuma sun tsere.

“Hakazalika, sojojin tare da hadin gwiwar jami’an sa-kai a ranar 22 ga watan Oktoba, sun kama wani mutum da ake zargi da mallakar katin zabe guda 67 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke garin Shuwari a karamar hukumar Maiduguri ta Jihar Borno.

“Haka kuma, a wannan sansani, an kashe wani sanannen dan ta’adda, Lawan Yashin, wanda ya yi yunkurin tserewa da ganin sojoji.

“A lokacin guda ‘yan ta’addar Boko Haram 145 da iyalansu da suka hada da manya maza 30, manya mata 33 da kananan yara 82 ne suka mika wuya ga sojoji a wurare daban-daban ga sojoji a Arewa maso Gabas,” in ji Danmadami.

A yankin Arewa maso Yamma, kakakin rundunar tsaron, ya ce dakarun hadin gwiwa na Hadarin Daji da Whirl Punch sun kashe ‘yan ta’adda 25, sun kama 18 tare da kubutar da fararen hula 19 a hare-hare daban-daban.

Mista Danmadami, ya ce sojojin sun kuma kwato manyan makamai da alburusai daban-daban da kuma shanu 441 da aka sace.

Ya kara da cewa sojojin a ranar 24 ga watan Oktoba, sun kai wa ‘yan ta’addan hari a kan hanyar Buruku-Angwan Yako-Udawa a karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka ceto fararen hula 10 tare da kwato motoci uku.

Kakakin rundunar, ya ce sojojin sun kuma kashe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wasu mutane tara da aka yi garkuwa da su a Faskari a Jihar Katsina da kuma Anka a Zamfara.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Tanzaniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.