Dakarun rundunar Sojin saman Nijeriya (NAF) sun lalata wasu mahimman wurareda suka kasance maboyar ‘yan ta’adda tare da daƙile wani harin da aka shirya kai wa yayin bukukuwan Sallah a jihar Borno.
Wata sanarwa daga mai magana da yawun NAF, Air Commodore Ehime, ta bayyana cewa hare-haren jiragen sama sun gudana tsakanin ranar 5 zuwa 6 ga watan Yuni, 2025.
A cewar sanarwar, an gudanar da wannan farmaki ne a ƙarƙashin Operation HADIN KAI, inda jiragen yakin suka kai hari kan sansanonin Boko Haram da ke Tumbumma Baba da Chira5lia a Kudancin yankin Tumbuns.
- Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan gg, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
- DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
An kai harin ne bisa sahihin bayanan sirri da suka nuna cewa gine-ginen da aka kai wa hari na ɗauke da kayan aiki da ake amfani da su wajen shirya hare-hare. Harin ya hana aiwatar da shirin barnar da ‘yan ta’addan suka yi niyya a lokacin bikin Sallah.
Ejodame ya ƙara da cewa wannan matakin gabanin lokaci ya nuna irin jajircewar NAF wajen kare rayukan fararen hula da tabbatar da tsaron kasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp