• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Su Wa Ke Da Hannu Wajen Badakalar Yaye Daliban Bogi A Jami’ar Kalaba?

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
1 year ago
in Ilimi
0
Su Wa Ke Da Hannu Wajen Badakalar Yaye Daliban Bogi A Jami’ar Kalaba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abin ne ya zama wani lamarin wanda zai ci gaba da daure kai,da daukar hankalin al’umma dangane da abubuwan da suke faruwa a jami’ar Kalaba babban birnin Jihar Kuros Ribas, saboda kuwa ba sau daya ba ne aka samu irin wannan ya fara faruwa a jami’ar ba. Ranar Litinin ce hukumar yi wa kasa hidima ta soke satifiket wadanda suka yi wa kasa hidima, tsakanin shekarun 2021 da 2023 wadanda daga jami’ar ne suka kammala karatunsu har suka tafi zuwa shirin yi wa kasa hidima na su 101 wadanda suka shiga jami’ar, har suka kammala ba tare da sun cika ka’idoji ba.

 

Abin da ke daure kai su wanene ke da alhaki na tantance wadanda suka cancanci shiga jami’ar, hukumar kula da lamurran masu yi wa kasa hidima ce, ko kuma ita jami’ar, saboda idan aka duba wadanda suka yi aikin yi wa kasa hidima tsakanin shekarun 2021 da 2023 har sun kai yawan hakan, suka shiga jami’ar har suka kammala suka yi aikin yi wa kasa hidima amma ba a gane ba sai da suka riga suka kammala. A wannan shekarar ma an dade da amincewa da 54, wadanda tuni aka tura sunayensu wuraren da ya dace su je su yi zaman wata guda, amma an gano cewar basu cancanci hakan ba. Duk daga ita jami’ar ta Kalaba.

  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura
  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

Gaba daya ke nan 155 wadanda suka halarci makarantar ta hanyar da bata kamata, suka kuma kammala ba a gano su ba, amma kuwa wannan lamari yana da ban mamaki. Me yake faruwa ne a ita jami’ar ta Kalaba sai kace ba Shugabnni? koda yake duk wannan ma somin tabi ne ko nace duk da zai dauki hankali, akwai ma wani wanda ke sayar da Biredi ya samu an sa sunan shi cikin wadanda za su tafi aikin yiwa kasa hdima da za a fara daga ranar 28 ga Agusta 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Ya kamata a jinjina wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima a karkashi shugabancin Birgediya Janar YD Ahmed irin jan aikin da take yin a kawo gyara ta bangaren ilimi, musamman ma yadda take tsayawa kai da fata sai taga ana yi abubuwan da suka dace kamar yadda doka ta shimfida. Bugu da kari duk a cikin irin kokarin nata ta gano makarantu masu bada HND basu bin ka’ida ta sai an yi aikin sanin mamaki ana shekara daya, kafin a samu damar zuwa karatiun HND. Wadanda suka kammala irin makarantun basu da satifiket mai nuna sun yi aikin sanin makama na shekara daya, na cikin tsaka mai wuya dangane da zuwa NYSC.

 

Mai lura da yadda harkokin jami’ar ta Kalaba suke tafiya ritaya DIG Udom Edppoudom ya gode wa mataimakiyar shugabar jami’ar Farfesa Florence Obi, akan irin matakin da ta dauka wajen zuwa ofishin ta bashi labari,inda ta ce ta ga wasu sunayen daliban da basu kamata ace suna cikin ‘yan makarantar ba. Ita kuma ce ta sanar da hukumar kula da al’amuran masu yiwa kasa hidima akan sunayen wadanda basu cancanta ace sun yi karatu a makarantar ba ,amma har sun kammala har ma an tura sunayensu Jihohin da za su tafi aikin yiwa kasa hidimar.

 

Lokaci ya yi wanda za a hukunta mutane 155 wadanda suka yi Jami’ar ta hanyar da bata dace ba, da wadanda suka taimaka masu har suka samu damar, domin hakan ya zama izina ga wadanda suke yi asirinsu bai kai ga tonuwa ba, da kuma wadanda suka fara tunanin yin hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (2)

Next Post

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

Related

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

4 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

6 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

1 week ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 week ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Next Post
Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.