ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Su Wa Ke Da Hannu Wajen Badakalar Yaye Daliban Bogi A Jami’ar Kalaba?

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
2 years ago
Kalaba

Abin ne ya zama wani lamarin wanda zai ci gaba da daure kai,da daukar hankalin al’umma dangane da abubuwan da suke faruwa a jami’ar Kalaba babban birnin Jihar Kuros Ribas, saboda kuwa ba sau daya ba ne aka samu irin wannan ya fara faruwa a jami’ar ba. Ranar Litinin ce hukumar yi wa kasa hidima ta soke satifiket wadanda suka yi wa kasa hidima, tsakanin shekarun 2021 da 2023 wadanda daga jami’ar ne suka kammala karatunsu har suka tafi zuwa shirin yi wa kasa hidima na su 101 wadanda suka shiga jami’ar, har suka kammala ba tare da sun cika ka’idoji ba.

 

Abin da ke daure kai su wanene ke da alhaki na tantance wadanda suka cancanci shiga jami’ar, hukumar kula da lamurran masu yi wa kasa hidima ce, ko kuma ita jami’ar, saboda idan aka duba wadanda suka yi aikin yi wa kasa hidima tsakanin shekarun 2021 da 2023 har sun kai yawan hakan, suka shiga jami’ar har suka kammala suka yi aikin yi wa kasa hidima amma ba a gane ba sai da suka riga suka kammala. A wannan shekarar ma an dade da amincewa da 54, wadanda tuni aka tura sunayensu wuraren da ya dace su je su yi zaman wata guda, amma an gano cewar basu cancanci hakan ba. Duk daga ita jami’ar ta Kalaba.

ADVERTISEMENT
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura
  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

Gaba daya ke nan 155 wadanda suka halarci makarantar ta hanyar da bata kamata, suka kuma kammala ba a gano su ba, amma kuwa wannan lamari yana da ban mamaki. Me yake faruwa ne a ita jami’ar ta Kalaba sai kace ba Shugabnni? koda yake duk wannan ma somin tabi ne ko nace duk da zai dauki hankali, akwai ma wani wanda ke sayar da Biredi ya samu an sa sunan shi cikin wadanda za su tafi aikin yiwa kasa hdima da za a fara daga ranar 28 ga Agusta 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Ya kamata a jinjina wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima a karkashi shugabancin Birgediya Janar YD Ahmed irin jan aikin da take yin a kawo gyara ta bangaren ilimi, musamman ma yadda take tsayawa kai da fata sai taga ana yi abubuwan da suka dace kamar yadda doka ta shimfida. Bugu da kari duk a cikin irin kokarin nata ta gano makarantu masu bada HND basu bin ka’ida ta sai an yi aikin sanin mamaki ana shekara daya, kafin a samu damar zuwa karatiun HND. Wadanda suka kammala irin makarantun basu da satifiket mai nuna sun yi aikin sanin makama na shekara daya, na cikin tsaka mai wuya dangane da zuwa NYSC.

 

Mai lura da yadda harkokin jami’ar ta Kalaba suke tafiya ritaya DIG Udom Edppoudom ya gode wa mataimakiyar shugabar jami’ar Farfesa Florence Obi, akan irin matakin da ta dauka wajen zuwa ofishin ta bashi labari,inda ta ce ta ga wasu sunayen daliban da basu kamata ace suna cikin ‘yan makarantar ba. Ita kuma ce ta sanar da hukumar kula da al’amuran masu yiwa kasa hidima akan sunayen wadanda basu cancanta ace sun yi karatu a makarantar ba ,amma har sun kammala har ma an tura sunayensu Jihohin da za su tafi aikin yiwa kasa hidimar.

 

Lokaci ya yi wanda za a hukunta mutane 155 wadanda suka yi Jami’ar ta hanyar da bata dace ba, da wadanda suka taimaka masu har suka samu damar, domin hakan ya zama izina ga wadanda suke yi asirinsu bai kai ga tonuwa ba, da kuma wadanda suka fara tunanin yin hakan.

Kalaba
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Kalaba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.