ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Su Wa Ke Da Hannu Wajen Badakalar Yaye Daliban Bogi A Jami’ar Kalaba?

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
2 years ago
Kalaba

Abin ne ya zama wani lamarin wanda zai ci gaba da daure kai,da daukar hankalin al’umma dangane da abubuwan da suke faruwa a jami’ar Kalaba babban birnin Jihar Kuros Ribas, saboda kuwa ba sau daya ba ne aka samu irin wannan ya fara faruwa a jami’ar ba. Ranar Litinin ce hukumar yi wa kasa hidima ta soke satifiket wadanda suka yi wa kasa hidima, tsakanin shekarun 2021 da 2023 wadanda daga jami’ar ne suka kammala karatunsu har suka tafi zuwa shirin yi wa kasa hidima na su 101 wadanda suka shiga jami’ar, har suka kammala ba tare da sun cika ka’idoji ba.

 

Abin da ke daure kai su wanene ke da alhaki na tantance wadanda suka cancanci shiga jami’ar, hukumar kula da lamurran masu yi wa kasa hidima ce, ko kuma ita jami’ar, saboda idan aka duba wadanda suka yi aikin yi wa kasa hidima tsakanin shekarun 2021 da 2023 har sun kai yawan hakan, suka shiga jami’ar har suka kammala suka yi aikin yi wa kasa hidima amma ba a gane ba sai da suka riga suka kammala. A wannan shekarar ma an dade da amincewa da 54, wadanda tuni aka tura sunayensu wuraren da ya dace su je su yi zaman wata guda, amma an gano cewar basu cancanci hakan ba. Duk daga ita jami’ar ta Kalaba.

ADVERTISEMENT
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura
  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

Gaba daya ke nan 155 wadanda suka halarci makarantar ta hanyar da bata kamata, suka kuma kammala ba a gano su ba, amma kuwa wannan lamari yana da ban mamaki. Me yake faruwa ne a ita jami’ar ta Kalaba sai kace ba Shugabnni? koda yake duk wannan ma somin tabi ne ko nace duk da zai dauki hankali, akwai ma wani wanda ke sayar da Biredi ya samu an sa sunan shi cikin wadanda za su tafi aikin yiwa kasa hdima da za a fara daga ranar 28 ga Agusta 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Ya kamata a jinjina wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima a karkashi shugabancin Birgediya Janar YD Ahmed irin jan aikin da take yin a kawo gyara ta bangaren ilimi, musamman ma yadda take tsayawa kai da fata sai taga ana yi abubuwan da suka dace kamar yadda doka ta shimfida. Bugu da kari duk a cikin irin kokarin nata ta gano makarantu masu bada HND basu bin ka’ida ta sai an yi aikin sanin mamaki ana shekara daya, kafin a samu damar zuwa karatiun HND. Wadanda suka kammala irin makarantun basu da satifiket mai nuna sun yi aikin sanin makama na shekara daya, na cikin tsaka mai wuya dangane da zuwa NYSC.

 

Mai lura da yadda harkokin jami’ar ta Kalaba suke tafiya ritaya DIG Udom Edppoudom ya gode wa mataimakiyar shugabar jami’ar Farfesa Florence Obi, akan irin matakin da ta dauka wajen zuwa ofishin ta bashi labari,inda ta ce ta ga wasu sunayen daliban da basu kamata ace suna cikin ‘yan makarantar ba. Ita kuma ce ta sanar da hukumar kula da al’amuran masu yiwa kasa hidima akan sunayen wadanda basu cancanta ace sun yi karatu a makarantar ba ,amma har sun kammala har ma an tura sunayensu Jihohin da za su tafi aikin yiwa kasa hidimar.

 

Lokaci ya yi wanda za a hukunta mutane 155 wadanda suka yi Jami’ar ta hanyar da bata dace ba, da wadanda suka taimaka masu har suka samu damar, domin hakan ya zama izina ga wadanda suke yi asirinsu bai kai ga tonuwa ba, da kuma wadanda suka fara tunanin yin hakan.

Kalaba
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kalaba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.