Lokacin da gwamnatin tarayya ta kafa babban birnin tarayya (FCT) da Hukumar Raya FCT (FCDA) a shekarar 1976, babu wata muhimmiyar cibiyar more rayuwa a cikin kowane gari na FCT; kamar makarantu, asibitoci, ruwan sha, layin waya, ofishin posta, wutar lantarki da sauran makamantansu. Don haka ne, aka kafa sansani ‘Field Base FCDA’ a Suleja. Haka kuma, an yi amfani da jami’an karamar hukumar, domin tallafa wa sabuwar hukumar FCDA ta tsaya da kafarta.
Malam Abdullahi Ladan ne aka dora wa nauyin rike mukamai biyu a lokaci guda, Sakataren Karamar Hukumar Abuja, kamar yadda ake kiransa a wancan lokaci, sannan kuma shi ne shugaban lissafi na farko na FCDA tun a shekarar 1976, kafin a kafa tsarin gudanarwar hukumar. Yanzu haka, shi ne Wazirin Zazzau na Suleja, yana kuma da shekaru 96, yanzu haka kuma yana kwance sakamakon rashin lafiya. Babban abin takaici shi ne, an manta da dukkanin irin gudummawar da ya bayar tun kafin ya bar duniya.
- Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai
- Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ofisoshin Sakataren Gudanarwa na farko da na biyu na FCDA da na Ministan FCT na farko, duk suna Suleja ne. A watan Yuni na 1977, FCDA ta ba da kwangilar tsara tsarin babban birnin Abuja ga kamfanin ‘International Planning Associates’ (IPA).
IPA ta kammala aikin tare da mika shi ga Sakataren Gudanarwa na FCDA, Marigayi Abubakar Koko, a ranar 15 ga Fabrairun 1979. A wannan lokaci ne kuma, gwamnatin tarayya ta nemi a sauya sunan garin Abuja, domin amfani da shi a matsayin sabon babban birnin tarayya, inda Masarautar ta amince ba tare da neman wani diyya ba.
Saboda haka, ya zama dole ga IPA ta rubuta wani karin bayani a shafin farko na tsarin Birnin Abuja cewa: “IPA ta samu sanarwa bayan buga wannan rahoto cewa; za a sauya sunan garin Abuja da ke Jihar Neja zuwa Suleja, don gujewa rudani da sabon sunan Babban Birnin Tarayya. Duk inda aka ambaci Abuja a cikin wannan rahoto, yana nufin tsohon garin Abuja.”
A gefe guda kuma, al’ummar yankin ne suka sadaukar da gonakinsu, domin amfanin jama’a wajen gina sansanin FCDA. An cimma yarjejeniya cewa; a karshen amfani da filin, za a mayar da shi ga al’umma. Malam Ladan, ya dage har aka tabbatar da wannan yarjejeniya a rubuce kuma Marigayi Abubakar Koko, Sakataren FCDA, ya sa hannu don kada a samu sabanin tarihi.
Amma duk da haka, ba a mika kadarar ba har zuwa shekarar 1987, bayan fafutukar kwato ta tsawon lokaci. Daga bisani kuma, aka mika ta ga kungiyar tsoffin sojoji ta Nijeriya (Nigerian Legion), bayan sun nemi haka. Abin bakin ciki, gwamnatin tarayya ta kara lissafa filin a matsayin daya daga cikin kadarorinta da za a sayar a zamanin mulkin Obasanjo.
Da ba a gano takardun da Marigayi Koko ya sa hannu a kansu daga cikin tsohuwar ajiyar Jihar Neja ba, da an kwace filin. Wannan kuwa sakamakon hangen nesa ne na Malam Ladan.
Bayan dawo da ikon filin a karo na biyu a ranar 30 ga Oktoba, 2007, al’umma suka mika filin ga Gwamnatin Jihar Neja, domin bai wa Jami’ar IBB ta jihar damar kafa reshe a Suleja. Amma fiye da shekara 17 da yin haka, Gwamnatin Neja ta kasa ware ko sisin kwabo don fara gina wannan reshe.
Abin takaici, tun bayan kirkiro Jihar Neja a 1975, babu wata jami’ar gaba da sakandire da gwamnatin jiha ko ta tarayya ta kafa a Masarautar Suleja, duk da koke-koke da dama, har ma da kiran da dan Majalisar Suleja ya yi kwanan nan a gaban majalisar jihar. Wasu sassan na jihar har suna alfahari da dama daga cikin irin wadannan cibiyoyi. Har da shirin kafa makarantar koyon aikin jinya a tsohon wurin makarantar jinya ta FCT a sansanin FCDA ya zama kawai na cin fuska ne kawai. Hakan na faruwa duk da cewa; akwai Cibiyar Lafiya ta Tarayya da aka ware domin Suleja, amma aka karkatar da ita zuwa wani gari a cikin jihar.
Yankin Masarautar Suleja, shi ne mafi tasiri a fannin tattalin arziki a Jihar Neja, saboda kusancinsa da babban birnin tarayya. Gwamnatin Jihar Neja, na ci gaba da cin moriyar hakan ta hanyar tara haraji masu tarin yawa kamar PAYE, kudin filaye da kadarori da sauran haraji. Masarautar Suleja ita kadai na ba da akalla kashi 40 cikin 100 na kudaden da jihar ke samu daga cikin gida. Kudaden harajin da ake tarawa daga Karamar Hukumar Suleja, sun fi na kowace karamar hukuma a jihar. A kwana-kwanan nan, gwamnan ya bayyana haka.
Amma fa, idan aka kwatanta da wasu garuruwa a cikin jihar, ingancin titin da ake ginawa a cikin birnin Suleja, bai kai kima ba ko kadan. Daga Maje zuwa Madalla, ana iya cewa kwangila ce ta biliyoyin Nairori. Amma kuma, babu wani allon kwangila da ke bayyana sunan dan kwangilar ko hukumar da ke sa ido. Wannan yana nuna irin gazawar da ake da ita wajen gaskiya da rikon amana cikin mulki.
Jama’ar Suleja da masu kaunar garin, ba su da wani zabin da ya wuce su saka a ransu cewa; wata boyayyar makarkashiya ce aka shirya, don rage kudin aikin domin amfanuwar wasu. Wannan kuwa, wata shaida ce ta yadda ake yi wa wanda ke kawo riba wulakanci. Abin takaici ne a ce garin da ke bayar da kudaden shiga ya zama wanda aka watsar da shi a fannin gine-gine da walwalar jama’a.
Za a ci gaba In Shaa Allah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp