• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi da ta gabata, fusatattun gwamnonin PDP da ake kira da G-5 sun gindaya sababbin sharudda kafin su goyi bayan Atiku Abubakar.

Wannan yana zuwa ne a daidai lokacin da tawagar dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suke zawarcin gwamnoni domin su mara musu baya a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba
  • Dalibi Ya Rataye Kansa Har Lahira Saboda Budurwarsa Ta Auri Wani A Gombe

Da suke jawabi jin kadan bayan ganawar sirri a Jihar Legas, gwamnonin sun bayyana cewa har yanzu kofar yin silhu da Atiku a bude take.

A wurin ganawar akwai gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde da gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP, Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni wadanda suka hada da Ayodele Fayose (Ekiti) da Donald Duke (Kuros Riba) da Olusegun Mimiko (Ondo) da kuma Jonah Jang (Filato).

Haka kuma akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Adoke da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Taofeek Arapaja da Sanata Nasif Suleiman da Sanata Sandy Onor da kuma Sanato Sam Ohabunwa.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ganawar ta gudana kwanaki kadan bayan gwamnaoni sun bayyana dan takarar gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara. Sun gudanar da irin wannan ganawa a Inugu da Benuwai da kuma kasashen ketare. Gwamnonin sun yi bore ga Atiku kan kin dakatar da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu.

Da yake magana a wurin ganawar, Makinde ya bayyana cewa shi da sauran abokanansa za su ci gaba da fafatuka har sai shugabannin jam’iyya da sauran dattawan jam’iyyar sun dawo daga hayyacinsu.

Ya ce, “Mun hadu ne a wannan wuri domin ganawa da sauran jiga-jigan jam’iyyar PDP. Mu ne gwamnonin guda biyar da ake kira G-5, wanda muka kasance sabuwar tawaga masu mutunci.

“Idan aka kallemu za a ga cewa gwamnoni ne guda biyar da suke ci gaba da fafatuka, kuma mu a yankin kudu maso yamma mun sake bibiyan al’amuran jam’iyyar domin ganin abubuwan da suke gudana game da zabe mai zuwa.”

Bayan ganawar sirrin, Jang ya jaddada cewa suna nan a kan matakansu kan abubuwan da suka tattauna a Fatakwal.

“Bayan nazari kan abubuwan da suke gudana a jam’iyyar, mun cimma matsaya kan yanke hukuncin da muka zantar a garin Fatakwal. Sannan mun gana a nan ne domin jaddada matsayarmu wajen bude kofar tattaunawa da jam’iyyarmu ta PDP,” in ji shi.

Gwamnonin sun gudanar da ganawar ce a dakin taro na George da ke Ikoyi, inda Wike ya bayyana cewa za su goyi bayan jam’iyyarsu a zabe mai zuwa matukar aka biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuG5PDPSharudaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Next Post

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.