• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi da ta gabata, fusatattun gwamnonin PDP da ake kira da G-5 sun gindaya sababbin sharudda kafin su goyi bayan Atiku Abubakar.

Wannan yana zuwa ne a daidai lokacin da tawagar dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suke zawarcin gwamnoni domin su mara musu baya a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba
  • Dalibi Ya Rataye Kansa Har Lahira Saboda Budurwarsa Ta Auri Wani A Gombe

Da suke jawabi jin kadan bayan ganawar sirri a Jihar Legas, gwamnonin sun bayyana cewa har yanzu kofar yin silhu da Atiku a bude take.

A wurin ganawar akwai gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde da gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP, Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni wadanda suka hada da Ayodele Fayose (Ekiti) da Donald Duke (Kuros Riba) da Olusegun Mimiko (Ondo) da kuma Jonah Jang (Filato).

Haka kuma akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Adoke da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Taofeek Arapaja da Sanata Nasif Suleiman da Sanata Sandy Onor da kuma Sanato Sam Ohabunwa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ganawar ta gudana kwanaki kadan bayan gwamnaoni sun bayyana dan takarar gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara. Sun gudanar da irin wannan ganawa a Inugu da Benuwai da kuma kasashen ketare. Gwamnonin sun yi bore ga Atiku kan kin dakatar da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu.

Da yake magana a wurin ganawar, Makinde ya bayyana cewa shi da sauran abokanansa za su ci gaba da fafatuka har sai shugabannin jam’iyya da sauran dattawan jam’iyyar sun dawo daga hayyacinsu.

Ya ce, “Mun hadu ne a wannan wuri domin ganawa da sauran jiga-jigan jam’iyyar PDP. Mu ne gwamnonin guda biyar da ake kira G-5, wanda muka kasance sabuwar tawaga masu mutunci.

“Idan aka kallemu za a ga cewa gwamnoni ne guda biyar da suke ci gaba da fafatuka, kuma mu a yankin kudu maso yamma mun sake bibiyan al’amuran jam’iyyar domin ganin abubuwan da suke gudana game da zabe mai zuwa.”

Bayan ganawar sirrin, Jang ya jaddada cewa suna nan a kan matakansu kan abubuwan da suka tattauna a Fatakwal.

“Bayan nazari kan abubuwan da suke gudana a jam’iyyar, mun cimma matsaya kan yanke hukuncin da muka zantar a garin Fatakwal. Sannan mun gana a nan ne domin jaddada matsayarmu wajen bude kofar tattaunawa da jam’iyyarmu ta PDP,” in ji shi.

Gwamnonin sun gudanar da ganawar ce a dakin taro na George da ke Ikoyi, inda Wike ya bayyana cewa za su goyi bayan jam’iyyarsu a zabe mai zuwa matukar aka biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuG5PDPSharudaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Next Post

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.