• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sulhu Da Atiku: Sabbin Sharruddan Da Fusatattun Gwamnonin PDP Suka Gindaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi da ta gabata, fusatattun gwamnonin PDP da ake kira da G-5 sun gindaya sababbin sharudda kafin su goyi bayan Atiku Abubakar.

Wannan yana zuwa ne a daidai lokacin da tawagar dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suke zawarcin gwamnoni domin su mara musu baya a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba
  • Dalibi Ya Rataye Kansa Har Lahira Saboda Budurwarsa Ta Auri Wani A Gombe

Da suke jawabi jin kadan bayan ganawar sirri a Jihar Legas, gwamnonin sun bayyana cewa har yanzu kofar yin silhu da Atiku a bude take.

A wurin ganawar akwai gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde da gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP, Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni wadanda suka hada da Ayodele Fayose (Ekiti) da Donald Duke (Kuros Riba) da Olusegun Mimiko (Ondo) da kuma Jonah Jang (Filato).

Haka kuma akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Adoke da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Taofeek Arapaja da Sanata Nasif Suleiman da Sanata Sandy Onor da kuma Sanato Sam Ohabunwa.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ganawar ta gudana kwanaki kadan bayan gwamnaoni sun bayyana dan takarar gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara. Sun gudanar da irin wannan ganawa a Inugu da Benuwai da kuma kasashen ketare. Gwamnonin sun yi bore ga Atiku kan kin dakatar da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu.

Da yake magana a wurin ganawar, Makinde ya bayyana cewa shi da sauran abokanansa za su ci gaba da fafatuka har sai shugabannin jam’iyya da sauran dattawan jam’iyyar sun dawo daga hayyacinsu.

Ya ce, “Mun hadu ne a wannan wuri domin ganawa da sauran jiga-jigan jam’iyyar PDP. Mu ne gwamnonin guda biyar da ake kira G-5, wanda muka kasance sabuwar tawaga masu mutunci.

“Idan aka kallemu za a ga cewa gwamnoni ne guda biyar da suke ci gaba da fafatuka, kuma mu a yankin kudu maso yamma mun sake bibiyan al’amuran jam’iyyar domin ganin abubuwan da suke gudana game da zabe mai zuwa.”

Bayan ganawar sirrin, Jang ya jaddada cewa suna nan a kan matakansu kan abubuwan da suka tattauna a Fatakwal.

“Bayan nazari kan abubuwan da suke gudana a jam’iyyar, mun cimma matsaya kan yanke hukuncin da muka zantar a garin Fatakwal. Sannan mun gana a nan ne domin jaddada matsayarmu wajen bude kofar tattaunawa da jam’iyyarmu ta PDP,” in ji shi.

Gwamnonin sun gudanar da ganawar ce a dakin taro na George da ke Ikoyi, inda Wike ya bayyana cewa za su goyi bayan jam’iyyarsu a zabe mai zuwa matukar aka biya musu bukatocinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuG5PDPSharudaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Next Post

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

Samun Man Fetur Ne Ya Kashe Masa-na’antunmu – Al-Mustapha

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.