• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, jiya Jumma’a 6 ga wata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. 

 

Baya ga wakilan kamfanonin kasar Sin, akwai kuma wakilan kamfanonin kasashen Afirka 48 da suka halarci taron, ciki har da na Senegal, da Afirka ta Kudu, da Kenya da sauransu, masu alaka da sana’o’i daban-daban.

  • Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano
  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

A wajen bikin kaddamar da taron, firaministan kasar Sin Li Qiang ya ba da shawarar cewa, ya dace Sin da Afirka su kara tuntubar juna ta fannin kasuwa, da kara yin mu’amalar sana’o’insu, da kuma kara karfin kirkire-kirkire.

 

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

A wajen taron kolin dandalin FOCAC na wannan karo, wato dandalin tattuna hadin-gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta ce, za ta hada kai tare da kasashen Afirka, don daukar wasu manyan matakan abokantaka guda 10 don zamanantar da kansu, inda a wannan sabon mafari, kamfanonin Sin da Afirka za su fuskanci karin damammakin hadin-gwiwa.

 

Ana samun damammaki daga mu’amalar tsare-tsaren sana’o’i iri-iri, al’amarin da ya kasance tushen hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci. Sin babbar kasa ce dake tasowa, wadda ke da cikakken tsarin sana’o’i iri-iri a duk fadin duniya, kana, Afirka, nahiya ce dake da dimbin kasashe masu tasowa da yawa a duniya. Don haka, bangarorin biyu za su iya yin hadin-gwiwa a tsarin sana’o’i da tsarin samar da kayayyaki.

 

Ana kuma samun damammaki da dama ta hanyar tattaro sabon kuzari. Tun daga habaka “kasuwancin hanyar siliki” cikin hadin-gwiwa, har zuwa motoci masu amfani da sabon makamashi, da na’urorin hasken rana, da na’urorin samar da wutar lantarki bisa karfin iska da kasar Sin ta kera, wadanda suka taimaka sosai ga ci gaban sabbin makamashi a Afirka, kasar Sin da kasashen Afirka suna gudanar da hadin-gwiwa sosai a fannonin tattalin arziki irin na zamani, da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

A cewar shugabannin kamfanonin Afirka da suka halarci taron, babban abun dake tattare da hadin-gwiwar Afirka da Sin shi ne yin kirkire-kirkire, kuma dabarun kasar Sin ta fannin sabon makamashi, da kera motoci masu amfani da lantarki sun cancanci Afirka ta yi koyi.

 

Kaza lika, ana samun damammaki daga ra’ayi iri daya da aka cimma wajen yin hadin-gwiwa. A wajen babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, shugabannin kamfanonin sun nuna matukar sha’awarsu ta karfafa hadin-gwiwa, al’amarin dake da babbar ma’ana, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar kalubalen ra’ayin ba da kariya, tare da samar da kuzari ga duniya wajen cimma moriya tare. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188

Next Post

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

15 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

16 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

17 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

18 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

19 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.