• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, jiya Jumma’a 6 ga wata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. 

 

Baya ga wakilan kamfanonin kasar Sin, akwai kuma wakilan kamfanonin kasashen Afirka 48 da suka halarci taron, ciki har da na Senegal, da Afirka ta Kudu, da Kenya da sauransu, masu alaka da sana’o’i daban-daban.

  • Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano
  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

A wajen bikin kaddamar da taron, firaministan kasar Sin Li Qiang ya ba da shawarar cewa, ya dace Sin da Afirka su kara tuntubar juna ta fannin kasuwa, da kara yin mu’amalar sana’o’insu, da kuma kara karfin kirkire-kirkire.

 

Labarai Masu Nasaba

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

A wajen taron kolin dandalin FOCAC na wannan karo, wato dandalin tattuna hadin-gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta ce, za ta hada kai tare da kasashen Afirka, don daukar wasu manyan matakan abokantaka guda 10 don zamanantar da kansu, inda a wannan sabon mafari, kamfanonin Sin da Afirka za su fuskanci karin damammakin hadin-gwiwa.

 

Ana samun damammaki daga mu’amalar tsare-tsaren sana’o’i iri-iri, al’amarin da ya kasance tushen hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci. Sin babbar kasa ce dake tasowa, wadda ke da cikakken tsarin sana’o’i iri-iri a duk fadin duniya, kana, Afirka, nahiya ce dake da dimbin kasashe masu tasowa da yawa a duniya. Don haka, bangarorin biyu za su iya yin hadin-gwiwa a tsarin sana’o’i da tsarin samar da kayayyaki.

 

Ana kuma samun damammaki da dama ta hanyar tattaro sabon kuzari. Tun daga habaka “kasuwancin hanyar siliki” cikin hadin-gwiwa, har zuwa motoci masu amfani da sabon makamashi, da na’urorin hasken rana, da na’urorin samar da wutar lantarki bisa karfin iska da kasar Sin ta kera, wadanda suka taimaka sosai ga ci gaban sabbin makamashi a Afirka, kasar Sin da kasashen Afirka suna gudanar da hadin-gwiwa sosai a fannonin tattalin arziki irin na zamani, da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

A cewar shugabannin kamfanonin Afirka da suka halarci taron, babban abun dake tattare da hadin-gwiwar Afirka da Sin shi ne yin kirkire-kirkire, kuma dabarun kasar Sin ta fannin sabon makamashi, da kera motoci masu amfani da lantarki sun cancanci Afirka ta yi koyi.

 

Kaza lika, ana samun damammaki daga ra’ayi iri daya da aka cimma wajen yin hadin-gwiwa. A wajen babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, shugabannin kamfanonin sun nuna matukar sha’awarsu ta karfafa hadin-gwiwa, al’amarin dake da babbar ma’ana, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar kalubalen ra’ayin ba da kariya, tare da samar da kuzari ga duniya wajen cimma moriya tare. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188

Next Post

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Related

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

5 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

8 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

8 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

19 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

20 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

21 hours ago
Next Post
Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.