• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, jiya Jumma’a 6 ga wata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. 

 

Baya ga wakilan kamfanonin kasar Sin, akwai kuma wakilan kamfanonin kasashen Afirka 48 da suka halarci taron, ciki har da na Senegal, da Afirka ta Kudu, da Kenya da sauransu, masu alaka da sana’o’i daban-daban.

  • Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano
  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

A wajen bikin kaddamar da taron, firaministan kasar Sin Li Qiang ya ba da shawarar cewa, ya dace Sin da Afirka su kara tuntubar juna ta fannin kasuwa, da kara yin mu’amalar sana’o’insu, da kuma kara karfin kirkire-kirkire.

 

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

A wajen taron kolin dandalin FOCAC na wannan karo, wato dandalin tattuna hadin-gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta ce, za ta hada kai tare da kasashen Afirka, don daukar wasu manyan matakan abokantaka guda 10 don zamanantar da kansu, inda a wannan sabon mafari, kamfanonin Sin da Afirka za su fuskanci karin damammakin hadin-gwiwa.

 

Ana samun damammaki daga mu’amalar tsare-tsaren sana’o’i iri-iri, al’amarin da ya kasance tushen hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci. Sin babbar kasa ce dake tasowa, wadda ke da cikakken tsarin sana’o’i iri-iri a duk fadin duniya, kana, Afirka, nahiya ce dake da dimbin kasashe masu tasowa da yawa a duniya. Don haka, bangarorin biyu za su iya yin hadin-gwiwa a tsarin sana’o’i da tsarin samar da kayayyaki.

 

Ana kuma samun damammaki da dama ta hanyar tattaro sabon kuzari. Tun daga habaka “kasuwancin hanyar siliki” cikin hadin-gwiwa, har zuwa motoci masu amfani da sabon makamashi, da na’urorin hasken rana, da na’urorin samar da wutar lantarki bisa karfin iska da kasar Sin ta kera, wadanda suka taimaka sosai ga ci gaban sabbin makamashi a Afirka, kasar Sin da kasashen Afirka suna gudanar da hadin-gwiwa sosai a fannonin tattalin arziki irin na zamani, da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

A cewar shugabannin kamfanonin Afirka da suka halarci taron, babban abun dake tattare da hadin-gwiwar Afirka da Sin shi ne yin kirkire-kirkire, kuma dabarun kasar Sin ta fannin sabon makamashi, da kera motoci masu amfani da lantarki sun cancanci Afirka ta yi koyi.

 

Kaza lika, ana samun damammaki daga ra’ayi iri daya da aka cimma wajen yin hadin-gwiwa. A wajen babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, shugabannin kamfanonin sun nuna matukar sha’awarsu ta karfafa hadin-gwiwa, al’amarin dake da babbar ma’ana, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar kalubalen ra’ayin ba da kariya, tare da samar da kuzari ga duniya wajen cimma moriya tare. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188

Next Post

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

8 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

9 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

10 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

11 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

12 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.