ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

An gudanar da babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, jiya Jumma’a 6 ga wata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. 

 

Baya ga wakilan kamfanonin kasar Sin, akwai kuma wakilan kamfanonin kasashen Afirka 48 da suka halarci taron, ciki har da na Senegal, da Afirka ta Kudu, da Kenya da sauransu, masu alaka da sana’o’i daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano
  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

A wajen bikin kaddamar da taron, firaministan kasar Sin Li Qiang ya ba da shawarar cewa, ya dace Sin da Afirka su kara tuntubar juna ta fannin kasuwa, da kara yin mu’amalar sana’o’insu, da kuma kara karfin kirkire-kirkire.

 

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

A wajen taron kolin dandalin FOCAC na wannan karo, wato dandalin tattuna hadin-gwiwar Sin da Afirka, kasar Sin ta ce, za ta hada kai tare da kasashen Afirka, don daukar wasu manyan matakan abokantaka guda 10 don zamanantar da kansu, inda a wannan sabon mafari, kamfanonin Sin da Afirka za su fuskanci karin damammakin hadin-gwiwa.

 

Ana samun damammaki daga mu’amalar tsare-tsaren sana’o’i iri-iri, al’amarin da ya kasance tushen hadin-gwiwar tattalin arziki da kasuwanci. Sin babbar kasa ce dake tasowa, wadda ke da cikakken tsarin sana’o’i iri-iri a duk fadin duniya, kana, Afirka, nahiya ce dake da dimbin kasashe masu tasowa da yawa a duniya. Don haka, bangarorin biyu za su iya yin hadin-gwiwa a tsarin sana’o’i da tsarin samar da kayayyaki.

 

Ana kuma samun damammaki da dama ta hanyar tattaro sabon kuzari. Tun daga habaka “kasuwancin hanyar siliki” cikin hadin-gwiwa, har zuwa motoci masu amfani da sabon makamashi, da na’urorin hasken rana, da na’urorin samar da wutar lantarki bisa karfin iska da kasar Sin ta kera, wadanda suka taimaka sosai ga ci gaban sabbin makamashi a Afirka, kasar Sin da kasashen Afirka suna gudanar da hadin-gwiwa sosai a fannonin tattalin arziki irin na zamani, da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

A cewar shugabannin kamfanonin Afirka da suka halarci taron, babban abun dake tattare da hadin-gwiwar Afirka da Sin shi ne yin kirkire-kirkire, kuma dabarun kasar Sin ta fannin sabon makamashi, da kera motoci masu amfani da lantarki sun cancanci Afirka ta yi koyi.

 

Kaza lika, ana samun damammaki daga ra’ayi iri daya da aka cimma wajen yin hadin-gwiwa. A wajen babban taron shugabannin kamfanonin kasar Sin da kasashen Afirka karo na 8, shugabannin kamfanonin sun nuna matukar sha’awarsu ta karfafa hadin-gwiwa, al’amarin dake da babbar ma’ana, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar kalubalen ra’ayin ba da kariya, tare da samar da kuzari ga duniya wajen cimma moriya tare. (Murtala Zhang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Lallasa Benin Da Ci 3-0 A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.