• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Tabbas Jami’an Tsaro Za Su Kare Jami’an Zabe Babu Haufi – Farfesa Yakubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daidai saura makonni biyu a gudanar da zaɓe, Shugaban Hukumar Zaɓe na Ƙasa Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar wa Shugabannin Jami’o’i cewa za a kare rayuka da lafiyar dukkan malaman da za su yi aikin zaɓe.

 

Yakubu ya ce INEC na aiki tare da dukkan ɓangarorin jami’an tsaro na faɗin ƙasar nan domin samar da cikakken tsaro ga ma’aikatan da za su yi aikin zaɓe a matakai daban-daban har matakai 10.

  • CBN Ya Tabbatarwa INEC Samun Wadatattun Takardun Naira Don Gudanar Da Zaben 2023

Daga saman jerin sunayen muƙaman masu aikin zaɓe akwai Babban Baturen Zaɓe na Jiha, Jami’an Tattara Sakamakon Zaɓe na Jihohi, Baturen Zaɓe da Mataimakin sa da kuma masu sa-idon da aka tantance yardar su kula da yadda ake gudanar da zaɓen. Akwai kuma ‘yan jarida, waɗanda su ma waɗanda aka tantance ne za su riƙa zagayawa ɗauko labaran abin da ke faruwa a rumfunan zaɓe da cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen.

 

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shugaban INEC ya ce an tanadi inshora ga duk wani ma’aikacin da aka tantance zai yi aikin zaɓe.

 

Shugabannin jami’o’i sun nuna wa Shugaban INEC abubuwan da su ke da damuwa a kai, a lokacin ganawar ta su a Hedikwatar Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa, wadda ke kusa da Hedikwatar INEC a Abuja, a ranar Alhamis.

Farfesa Yakubu

Yakubu ne dai ya nemi a yi ganawar domin nan amincewa a ɗauki sunayen malaman jami’o’i da za su yi aikin zaɓe.

 

Sai dai wasu shugabannin jami’o’in sun nuna ɗar-ɗar dangane da matsalar tsaro a wasu yankunan da za a tura wasu malaman a wuraren da ba cikin birane ba.

 

A nan, Yakubu ya tabbatar masu da cewa a ko’ina har a cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.

 

Ya ce ya gana da shugabannin ɓangarorin tsaro na ƙasar nan, kuma sun tabbatar masa da cewa za su samar da isasshen tsaro.

Farfesa Yakubu

“Za mu yi aiki ne tare da ma’aikatan tsaro, kuma sun tabbatar min cewa za su samar da isasshen tsaro.

 

Yakubu ya ce za a fara horas da malaman jami’o’i aikin zaɓe a ranakun 21 da 22 ga Fabrairu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Maida Martani Game Da Shakkun Da Ake Mata Dangane Da Fashewar Bututun Nord Stream

Next Post

Wani Ya Rasu Yayin Da Magoya Bayan APC Da PDP Suka Yi Arangama Da Juna A Jigawa

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

11 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

16 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

17 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

18 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

19 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

20 hours ago
Next Post
Wani Ya Rasu Yayin Da Magoya Bayan APC Da PDP Suka Yi Arangama Da Juna A Jigawa

Wani Ya Rasu Yayin Da Magoya Bayan APC Da PDP Suka Yi Arangama Da Juna A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.