• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Tattalin Arzikin Sin Zai Habaka Kuma Duniya Za Ta Amfana

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Tabbas Tattalin Arzikin Sin Zai Habaka Kuma Duniya Za Ta Amfana

default

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rawar da kasar Sin ke takawa a duniya a fagen ci gaban tattalin arziki ba a boye take ba bisa yadda masana daga sassa daban-daban suke bayar da shaida a kai.

Kamar yadda kasar ta tsara samun bunkasar tattalin arziki da kashi 5% kuma aka ga nasarar haka a sarari a shekarar 2023, a bana ma gwamnatin kasar Sin ta kuduri aniyar cimma kason a shekarar 2024.

Masana tattalin arziki da manyan ‘yan kasuwa sun yi amannar cewa gwamnatin ta Sin ta tsara cimma wannan kaso ne daidai da al’amuran dake gudana a bangaren ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma hangen nesan gwamnatin wajen tafiyar da kasa.

Firaministan kasar Sin, Li Qiang wanda ya sanar da muradin da kasar take son cimmawa a farkon makon, a yayin da ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a gun taron bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar, inda ya nuna cewa, tabbas kasar za ta cimma muradinta yadda take so saboda damammakin da take da su na ci gaban tattalin arziki tun daga kan masana’antu da kasuwanni da ma’aikata da kuma kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 

A wani bangare na tsare-tsarenta, kasar Sin ta kara kasafin kudinta na shekara-shekara a bangaren kimiyya da fasaha da kashi 10% zuwa Yuan biliyan 370.8 da ba a taba ganin irinsa ba, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 51.6, wanda ya kasance mafi girma tun daga shekarar 2019.
“Za mu yi kokari cikin hanzari don habaka dogaro da kai da kara karfi a fannin kimiyya da fasaha,” in ji Li, “Za mu yi cikakken amfani da tagomashin da ke cikin sabon tsarin don samar da albarkatun kasa a duk fadin kasar don daukaka matsayin Sin a sashen kirkire-kirkire daban-daban.”

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Abubuwan da Firaminista Li ya bayyana, sun samu hujjoji da kawar da shakku daga bayanan wani masanin tattalin arziki da ci gaba a Jami’ar Columbia, Farfesa Jeffrey Sachs yayin da ya ce, “kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da Sin ke zurfafa kokari a kai suna samun bunkasa cikin hanzari kuma wannan ne zai dora kasar Sin a wani gawurtaccen matsayi a duniya nan da ‘yan shekaru masu zuwa.”

Har ila yau, don jawo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje, rahoton aikin gwamnati na wannan shekara ya gabatar da wasu matakai na musamman kamar ci gaba da rage tarnakin da kasashen waje suka fuskanta wajen zuba jari a kasar Sin.

Mataimakin shugaban kamfanin kere-kere na Panasonic dake Japan, Tetsuro Homma da shugaban sashen kayayyaki na kamfanin L’Oreal, Alexis Perakis-Valat, duk sun yi amannar cewa, fagen kasuwanci na kasar Sin na da matukar ban sha’awa tare da bayyana muradin fadada kasuwancinsu a kasar.

Bunkasar tattalin arzikin Sin ba ita kadai zai amfanar ba, har da sauran kasashen duniya, kasancewarta kashin bayan gudanar da hada-hada a duniya. Ko a shekarar 2023, ta ba da gudunmawa ga habakar tattalin arzikin duniya da kashi 32%, kamar yadda Majalisar Harkokin Kudi ta Kasa da Kasa ta bayyana.

Bugu da kari, wani bincike na Asusun Ba Da Lamuni na Duniya (IMF) ya nunar da cewa, ci gaban tattalin arzikin Sin ba ita kadai yake amfanarwa ba har da sauran duniya. Idan ta samu ci gaba da kashi daya, a kalla na sauran kasashe ya kan habaka da kashi 0.3.

Irin wannan kokari na Sin duk mutane na-gari ke fatan gani a duniya, ba kamar Amurka mai habaka cinikin makamai da danniya ga marasa karfi ba kamar yadda muke gani a Gaza da kasashen Afirka dake fama da karairayewar darajar kudi. Ko a bana, Amurka ta ba da izinin a ware wa bangaren tsaronta dala biliyan 886, an samu karin kusan kashi 3% daga na bara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAmurkaBunkasa Tattalin ArzikiCi GabaDuniyaMasanaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

CPPCC Ya Rufe Cikakken Taronsa Na Shekara-shekara 

Next Post

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

4 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 week ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.