ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Tattalin Arzikin Sin Zai Habaka Kuma Duniya Za Ta Amfana

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
default

default

Rawar da kasar Sin ke takawa a duniya a fagen ci gaban tattalin arziki ba a boye take ba bisa yadda masana daga sassa daban-daban suke bayar da shaida a kai.

Kamar yadda kasar ta tsara samun bunkasar tattalin arziki da kashi 5% kuma aka ga nasarar haka a sarari a shekarar 2023, a bana ma gwamnatin kasar Sin ta kuduri aniyar cimma kason a shekarar 2024.

Masana tattalin arziki da manyan ‘yan kasuwa sun yi amannar cewa gwamnatin ta Sin ta tsara cimma wannan kaso ne daidai da al’amuran dake gudana a bangaren ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma hangen nesan gwamnatin wajen tafiyar da kasa.

ADVERTISEMENT

Firaministan kasar Sin, Li Qiang wanda ya sanar da muradin da kasar take son cimmawa a farkon makon, a yayin da ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a gun taron bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar, inda ya nuna cewa, tabbas kasar za ta cimma muradinta yadda take so saboda damammakin da take da su na ci gaban tattalin arziki tun daga kan masana’antu da kasuwanni da ma’aikata da kuma kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 

A wani bangare na tsare-tsarenta, kasar Sin ta kara kasafin kudinta na shekara-shekara a bangaren kimiyya da fasaha da kashi 10% zuwa Yuan biliyan 370.8 da ba a taba ganin irinsa ba, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 51.6, wanda ya kasance mafi girma tun daga shekarar 2019.
“Za mu yi kokari cikin hanzari don habaka dogaro da kai da kara karfi a fannin kimiyya da fasaha,” in ji Li, “Za mu yi cikakken amfani da tagomashin da ke cikin sabon tsarin don samar da albarkatun kasa a duk fadin kasar don daukaka matsayin Sin a sashen kirkire-kirkire daban-daban.”

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Abubuwan da Firaminista Li ya bayyana, sun samu hujjoji da kawar da shakku daga bayanan wani masanin tattalin arziki da ci gaba a Jami’ar Columbia, Farfesa Jeffrey Sachs yayin da ya ce, “kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da Sin ke zurfafa kokari a kai suna samun bunkasa cikin hanzari kuma wannan ne zai dora kasar Sin a wani gawurtaccen matsayi a duniya nan da ‘yan shekaru masu zuwa.”

Har ila yau, don jawo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje, rahoton aikin gwamnati na wannan shekara ya gabatar da wasu matakai na musamman kamar ci gaba da rage tarnakin da kasashen waje suka fuskanta wajen zuba jari a kasar Sin.

Mataimakin shugaban kamfanin kere-kere na Panasonic dake Japan, Tetsuro Homma da shugaban sashen kayayyaki na kamfanin L’Oreal, Alexis Perakis-Valat, duk sun yi amannar cewa, fagen kasuwanci na kasar Sin na da matukar ban sha’awa tare da bayyana muradin fadada kasuwancinsu a kasar.

Bunkasar tattalin arzikin Sin ba ita kadai zai amfanar ba, har da sauran kasashen duniya, kasancewarta kashin bayan gudanar da hada-hada a duniya. Ko a shekarar 2023, ta ba da gudunmawa ga habakar tattalin arzikin duniya da kashi 32%, kamar yadda Majalisar Harkokin Kudi ta Kasa da Kasa ta bayyana.

Bugu da kari, wani bincike na Asusun Ba Da Lamuni na Duniya (IMF) ya nunar da cewa, ci gaban tattalin arzikin Sin ba ita kadai yake amfanarwa ba har da sauran duniya. Idan ta samu ci gaba da kashi daya, a kalla na sauran kasashe ya kan habaka da kashi 0.3.

Irin wannan kokari na Sin duk mutane na-gari ke fatan gani a duniya, ba kamar Amurka mai habaka cinikin makamai da danniya ga marasa karfi ba kamar yadda muke gani a Gaza da kasashen Afirka dake fama da karairayewar darajar kudi. Ko a bana, Amurka ta ba da izinin a ware wa bangaren tsaronta dala biliyan 886, an samu karin kusan kashi 3% daga na bara.

Sin
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.