ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Tattalin Arzikin Sin Zai Habaka Kuma Duniya Za Ta Amfana

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
default

default

Rawar da kasar Sin ke takawa a duniya a fagen ci gaban tattalin arziki ba a boye take ba bisa yadda masana daga sassa daban-daban suke bayar da shaida a kai.

Kamar yadda kasar ta tsara samun bunkasar tattalin arziki da kashi 5% kuma aka ga nasarar haka a sarari a shekarar 2023, a bana ma gwamnatin kasar Sin ta kuduri aniyar cimma kason a shekarar 2024.

Masana tattalin arziki da manyan ‘yan kasuwa sun yi amannar cewa gwamnatin ta Sin ta tsara cimma wannan kaso ne daidai da al’amuran dake gudana a bangaren ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma hangen nesan gwamnatin wajen tafiyar da kasa.

ADVERTISEMENT

Firaministan kasar Sin, Li Qiang wanda ya sanar da muradin da kasar take son cimmawa a farkon makon, a yayin da ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a gun taron bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar, inda ya nuna cewa, tabbas kasar za ta cimma muradinta yadda take so saboda damammakin da take da su na ci gaban tattalin arziki tun daga kan masana’antu da kasuwanni da ma’aikata da kuma kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 

A wani bangare na tsare-tsarenta, kasar Sin ta kara kasafin kudinta na shekara-shekara a bangaren kimiyya da fasaha da kashi 10% zuwa Yuan biliyan 370.8 da ba a taba ganin irinsa ba, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 51.6, wanda ya kasance mafi girma tun daga shekarar 2019.
“Za mu yi kokari cikin hanzari don habaka dogaro da kai da kara karfi a fannin kimiyya da fasaha,” in ji Li, “Za mu yi cikakken amfani da tagomashin da ke cikin sabon tsarin don samar da albarkatun kasa a duk fadin kasar don daukaka matsayin Sin a sashen kirkire-kirkire daban-daban.”

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Abubuwan da Firaminista Li ya bayyana, sun samu hujjoji da kawar da shakku daga bayanan wani masanin tattalin arziki da ci gaba a Jami’ar Columbia, Farfesa Jeffrey Sachs yayin da ya ce, “kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da Sin ke zurfafa kokari a kai suna samun bunkasa cikin hanzari kuma wannan ne zai dora kasar Sin a wani gawurtaccen matsayi a duniya nan da ‘yan shekaru masu zuwa.”

Har ila yau, don jawo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje, rahoton aikin gwamnati na wannan shekara ya gabatar da wasu matakai na musamman kamar ci gaba da rage tarnakin da kasashen waje suka fuskanta wajen zuba jari a kasar Sin.

Mataimakin shugaban kamfanin kere-kere na Panasonic dake Japan, Tetsuro Homma da shugaban sashen kayayyaki na kamfanin L’Oreal, Alexis Perakis-Valat, duk sun yi amannar cewa, fagen kasuwanci na kasar Sin na da matukar ban sha’awa tare da bayyana muradin fadada kasuwancinsu a kasar.

Bunkasar tattalin arzikin Sin ba ita kadai zai amfanar ba, har da sauran kasashen duniya, kasancewarta kashin bayan gudanar da hada-hada a duniya. Ko a shekarar 2023, ta ba da gudunmawa ga habakar tattalin arzikin duniya da kashi 32%, kamar yadda Majalisar Harkokin Kudi ta Kasa da Kasa ta bayyana.

Bugu da kari, wani bincike na Asusun Ba Da Lamuni na Duniya (IMF) ya nunar da cewa, ci gaban tattalin arzikin Sin ba ita kadai yake amfanarwa ba har da sauran duniya. Idan ta samu ci gaba da kashi daya, a kalla na sauran kasashe ya kan habaka da kashi 0.3.

Irin wannan kokari na Sin duk mutane na-gari ke fatan gani a duniya, ba kamar Amurka mai habaka cinikin makamai da danniya ga marasa karfi ba kamar yadda muke gani a Gaza da kasashen Afirka dake fama da karairayewar darajar kudi. Ko a bana, Amurka ta ba da izinin a ware wa bangaren tsaronta dala biliyan 886, an samu karin kusan kashi 3% daga na bara.

Sin
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Tanzania

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.