ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

by CGTN Hausa
2 years ago
Korea

Bayan dakatarwa ta sama da shekaru 4, a farkon wannan mako an gudanar da taron shugabannin kasashen Sin da Japan da Korea ta Kudu. Kuma yayin jawabin da ya gabatar ga taron harkokin kasuwanci karo na 8 tsakanin kasashen uku, firaministan Sin Li Qiang ya bukaci kasashen su dakile duk wani kutse daga waje da zai illata dangantakarsu.

Hakika, lokacin da aka shafe ba tare da gudanar da taron kasashen 3 ba, ya nuna tsanani da kuma girman yadda wasu kasashe daga waje ke tsoma baki cikin harkokin wadannan makwabta, lamarin da za a iya cewa bai amfani yankin da komai ba sai tankiya. Kasancewar Sin da Japan da Korea ta kudu matsayin makwabta, abu ne mai muhimmanci dake tattare da dimbin damarmaki. Kasashen dake makwabtaka da juna da kamanceceniyar al’adu, na da damarmakin raya kansu cikin aminci da girmama juna, idan har suka toshe kutse daga waje. A ganina, ci gaban daya daga cikinsu, nasara ce ga dukkansu, domin abu ne da kowannensu zai iya cin gajiyarsa. Kana kyautatuwar dangantaka a tsakaninsu, ita ce za ta bunkasa musaya da fahimtar juna tsakanin jama’arsu, wanda zai kai ga samun al’ummomi masu jituwa dake zaune lafiya, kuma ’yan uwa juna.

  • Tsawon Hanyoyin Mota Da Sin Ta Shimfida A Kauyuka Ya Karu Da Kashi 18.5% A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2 Daga Daliban Da Suka Sace A Kogi

Hadin gwiwa tsakanin bangarorin 3 shi ne zai ba su damar kara fahimtar juna da dinke duk wata baraka ko sabanin da za a iya samu a tsakaninsu. Bai kamata wasu daga cikinsu su rika barin wasu daga waje na tsoma baki cikin harkokinsu, ko jan ragamar harkokin da su ta shafa ba. Mai daki aka ce, shi ya san inda yake masa yoyo. Don haka, babu wata kasa daga waje da za ta fi su sanin yanayin da suke ciki da kuma bukatun da suke da shi, haka kuma babu wata daga waje da za ta fi su iya warware sabaninsu da kuma samar musu da hanyar raya kansu. Barin wata kasa tana hure musu kunne, tamkar tsaiko ne ga cikakken ’yancin da suke da shi a matsayinsu na kasashe.

ADVERTISEMENT

Ci gaban yankin da kwanciyar hankalinsa, ya dogara ne ga yunkurin kasashen Korea ta Kudu da Japan na kare cikakken ’yancin kansu, ta hanyar toshe duk wata kafa ta tsoma baki cikin harkokin yankin da kuma sanya muradun yankin a gaban komai. Kowa dai ya san kasar Sin kasa ce dake tabbatar da cikakken ikonta, kuma ba ’yar amshin shata ba ce, haka kuma ba ta tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe.

Fatan ita ce, kasashen Korea ta Kudu da Japan za su gyara kuskurensu, su sanya muradun al’ummominsu da na makwabtansu gaba da komai, kana su yi hadin gwiwa bisa gaskiya da girmama juna domin tabbatar da ci gaban yankin da ma kwanciyar hankalinsa.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

A shekarar 1999, shugabannin kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu sun fara yunkurin hadin gwiwa tsakanin kasashen uku, a yayin da suka halarci taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen kudu maso gabashin Asiya ta ASEAN, da na kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu. Ya zuwa yanzu, shekaru 25 ke nan, kuma cikin wadannan shekarun da suka gabata, hadin gwiwa tsakanin kasashen uku ta bunkasa cikin yanayin sauye-sauye, ta kuma ba da muhimmiyar gudummawa ga bunkasuwar tattalin arzikin yankin, da ma kasashen duniya baki daya, ta kuma ba da jagoranci ga dunkulewar yankin baki daya.

Manazarta na ganin cewa, a halin yanzu, ana fuskantar yanayin sauye-sauye a kasashen duniya, an kuma kasa samun farfadowar tattalin arziki kamar yadda ake fata. Taron ganawar shugabannin kasashen Sin, da Japan da Koriya ta Kudu na wannan karo, ya nuna kyakkyawan fatan kasashen uku, ta fuskar habaka hadin gwiwarsu, da kuma daidaito tsakanin kasashen Japan da Koriya ta Kudu, kan manufofinsu masu nasaba da kasar Sin, da sassauta yanayin siyasa a tsakanin kasashen uku.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

Tabbatar Da Cikakken ’Yancin Kai, Ita Ce Za Ta Kyautata Dangantakar Sin Da Japan Da Korea Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.