• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafiya Da Gwani Mai Dadi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tafiya Da Gwani Mai Dadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasashen Afirka ke kara nuna amincewa da kasar Sin a fannonin hadin gwiwar wanzar da ci gabansu, karin kasashen nahiyar na dada zurfafa hadin gwiwa, da bunkasa ci gaban alakar dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Hakan ne ma ya sa a baya bayan nan shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, yayin da yake karbar takardar kama aiki daga sabon jakadan Sin a kasar sa Zhou Ding, ya jaddada burinsa na fadada hadin kai da bangaren kasar Sin a fannoni daban daban.

  • Xi Jinping Ya Nanata Muhimmancin Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ga duk mai bibbiyar yanayin alakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe, ya kwana da sanin yadda Sin din ta jima tana tallafawa Zimbabwe wajen samar da ababen more rayuwa, ta hanyar samar da kudaden gudanar da manyan ayyukan raya kasa, ciki har da katafaren ginin ofishin majalissar dokokin kasar, da fadada tashar samar da lantarki ta tururi mai zafi, da sake fasali, da kuma fadada babban filin jiragen sama na Robert Mugabe, da zango na uku na aikin samar da hidimar wayar salula ga al’ummar kasar, ayyukan da suka yi matukar taka rawar gani a fannin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Zimbabwe.

Bahaushe kan ce “Tafiya da gwani mai dadi”. A gani na hakan ne ma ya sanya kasashe masu tasowa ke dada fifita alakar su da Sin, idan ana batun alakar kasa da kasa, kasancewar kasar Sin na nacewa manufar kaucewa tsoma baki cikin harkokin wajen sauran kasashe, da nuna adawa da takunkuman da kasashen yamma ke kakabawa sauran kasashe, ciki har da irin wadanda aka kakabawa kasar ta Zimbabwe.

Baya ga haka, kasar Sin ta yi cudanya, tare da mara baya ga kasashen Afirka, a fannin samar da tallafin yaki da annobar COVID-19 wadda a ’yan shekarun da suka gabata ta addabi duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Hakan ne ma ya sa masharhanta da yawa ke hasashen kara kyautatuwa, da yaukaka, da dorewar alakar Sin da abokan tafiyarta wato kasashe masu tasowa, wadanda suka amince su yi tafiya kafada da kafada da Sin din bisa mutunta juna, da zurfafa musaya a fannonin hadin gwiwa daban daban, karkashin manufofi irin na “Shawarar ziri daya da hanya daya”, da manufar bunkasa ci gaban duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Rusashshiyar Kungiyar G-5

Next Post

Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

8 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

8 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

9 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

10 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

11 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

12 hours ago
Next Post
Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Isra'ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa 'Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.