• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafiya Da Gwani Mai Dadi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tafiya Da Gwani Mai Dadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasashen Afirka ke kara nuna amincewa da kasar Sin a fannonin hadin gwiwar wanzar da ci gabansu, karin kasashen nahiyar na dada zurfafa hadin gwiwa, da bunkasa ci gaban alakar dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Hakan ne ma ya sa a baya bayan nan shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, yayin da yake karbar takardar kama aiki daga sabon jakadan Sin a kasar sa Zhou Ding, ya jaddada burinsa na fadada hadin kai da bangaren kasar Sin a fannoni daban daban.

  • Xi Jinping Ya Nanata Muhimmancin Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ga duk mai bibbiyar yanayin alakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe, ya kwana da sanin yadda Sin din ta jima tana tallafawa Zimbabwe wajen samar da ababen more rayuwa, ta hanyar samar da kudaden gudanar da manyan ayyukan raya kasa, ciki har da katafaren ginin ofishin majalissar dokokin kasar, da fadada tashar samar da lantarki ta tururi mai zafi, da sake fasali, da kuma fadada babban filin jiragen sama na Robert Mugabe, da zango na uku na aikin samar da hidimar wayar salula ga al’ummar kasar, ayyukan da suka yi matukar taka rawar gani a fannin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Zimbabwe.

Bahaushe kan ce “Tafiya da gwani mai dadi”. A gani na hakan ne ma ya sanya kasashe masu tasowa ke dada fifita alakar su da Sin, idan ana batun alakar kasa da kasa, kasancewar kasar Sin na nacewa manufar kaucewa tsoma baki cikin harkokin wajen sauran kasashe, da nuna adawa da takunkuman da kasashen yamma ke kakabawa sauran kasashe, ciki har da irin wadanda aka kakabawa kasar ta Zimbabwe.

Baya ga haka, kasar Sin ta yi cudanya, tare da mara baya ga kasashen Afirka, a fannin samar da tallafin yaki da annobar COVID-19 wadda a ’yan shekarun da suka gabata ta addabi duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Hakan ne ma ya sa masharhanta da yawa ke hasashen kara kyautatuwa, da yaukaka, da dorewar alakar Sin da abokan tafiyarta wato kasashe masu tasowa, wadanda suka amince su yi tafiya kafada da kafada da Sin din bisa mutunta juna, da zurfafa musaya a fannonin hadin gwiwa daban daban, karkashin manufofi irin na “Shawarar ziri daya da hanya daya”, da manufar bunkasa ci gaban duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Rusashshiyar Kungiyar G-5

Next Post

Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

17 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

18 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

20 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

20 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

22 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

24 hours ago
Next Post
Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Isra'ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa 'Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.