• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimakon Kasar Sin Na Ingiza Ci Gaba A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Kafofin yada labarai a kasar Habasha sun ruwaito a jiya cewa, yankin masana’antu na Kombolcha (KIP) da kasar Sin ta gina a kasar, ya samar da kimanin dala miliyan 28 na kudin shiga daga fiton kayayyaki zuwa ketare, cikin watannin 9 na farkon shekarar kudi ta kasar ta (2023/2024) da ta fara daga ranar 8 ga watan Yulin 2023.

Wannan ci gaba abun burgewa ne matuka, ganin yadda dukkan abubuwan da aka fitar, an samar da su ne a harabar yankin na KIP na kasar Habasha. Samar da yankin da kamfanin CCECC na kasar Sin ya gina, wani bangare ne na burin Habasha na zama cibiyar samar da kayayyaki a nahiyar Afrika, kuma da alama ta dauki hanyar cimma wannan buri nata, da taimakon kasar Sin.

  • Sin Ba Ta Da Masaniya Game Da Dalilin Philippines Na Kin Amincewa Da Daidaiton Da Aka Cimma Kan Batun Sashen Tudun Ruwa Na Ren’aijiao
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Yayin da ake fama da hauhawar farashin kayayyaki da ma raguwar darajar kudaden kasashe musamman na Afrika, masana na cewa samar da kayayyaki a cikin gida, wata ingantacciyar dabara ce ta shawo kan matsaloli da dama. Tabbas Habasha ta samarwa kanta mafita, godiya ga kasar Sin. Zan bada misali da wasu batutuwa 3.

Na farko, samar da kayayyaki a cikin gida. Yadda wannan yanki na KIP ke samar da kayayyaki a cikin gida, tabbas zai ragewa al’ummar kasar radadin hauhawar farashin kayayyaki. Ba su kadai ba ma, har da kasashe makwabta da nahiyar baki daya. Wannan lamari zai kara inganta kyautata rayuwar jama’a.

Na biyu, fiton kayayyaki. Wannan zai bunkasa karfin kasar na shiga kasuwannin duniya da ma kara haskata a dandalin kasa da kasa. Haka kuma zai kai ga bunkasa lamarin da zai bata karin damarmakin samun karin ci gaba ta fuskar kasuwanci da ababen more rayuwa tare da janyo jarin waje.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Na uku, samar da guraben ayyukan yi. Cikin watannin 9, wannan yankin masana’atu da Sin ta gina, ya samar da karin guraben ayyukan yi sama da 850 ga mazauna wurin. Daya daga cikin manyan abubuwan dake haifar da rashin ci gaba kasa da ma rikice-rikice shi ne yawaitar masu zaman kashe wando, amma da zarar aka samu ayyukan yi, to ya kan toshe kafofi da dama masu tarnaki ga ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al’umma.

A ganina, dangatakar Sin da kasar Habasha, ba samar da hanyar bunkasa tattalin arziki kadai ta yi ba, har ma da samarwa kasar irin dabarar kasar Sin ta samun ci gaba. Mun sani cewa, kasar Sin ta bullo da wata sabuwar hanyar ci gaba da ba a taba gani ba a duniya, inda take juya yawan al’umma da albarkatun da take da su a cikin gida zuwa hanyoyin bunaksa ci gabanta ba tare da mulkin mallaka ba. Hakika hulda da kasar Sin alheri ce, kuma na yi imanin sauran kasashen Afrika za su iya bin sawun Habasha don tabbatar da ci gabansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.