ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimakon Kasar Sin Na Ingiza Ci Gaba A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Kafofin yada labarai a kasar Habasha sun ruwaito a jiya cewa, yankin masana’antu na Kombolcha (KIP) da kasar Sin ta gina a kasar, ya samar da kimanin dala miliyan 28 na kudin shiga daga fiton kayayyaki zuwa ketare, cikin watannin 9 na farkon shekarar kudi ta kasar ta (2023/2024) da ta fara daga ranar 8 ga watan Yulin 2023.

Wannan ci gaba abun burgewa ne matuka, ganin yadda dukkan abubuwan da aka fitar, an samar da su ne a harabar yankin na KIP na kasar Habasha. Samar da yankin da kamfanin CCECC na kasar Sin ya gina, wani bangare ne na burin Habasha na zama cibiyar samar da kayayyaki a nahiyar Afrika, kuma da alama ta dauki hanyar cimma wannan buri nata, da taimakon kasar Sin.

  • Sin Ba Ta Da Masaniya Game Da Dalilin Philippines Na Kin Amincewa Da Daidaiton Da Aka Cimma Kan Batun Sashen Tudun Ruwa Na Ren’aijiao
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Yayin da ake fama da hauhawar farashin kayayyaki da ma raguwar darajar kudaden kasashe musamman na Afrika, masana na cewa samar da kayayyaki a cikin gida, wata ingantacciyar dabara ce ta shawo kan matsaloli da dama. Tabbas Habasha ta samarwa kanta mafita, godiya ga kasar Sin. Zan bada misali da wasu batutuwa 3.

ADVERTISEMENT

Na farko, samar da kayayyaki a cikin gida. Yadda wannan yanki na KIP ke samar da kayayyaki a cikin gida, tabbas zai ragewa al’ummar kasar radadin hauhawar farashin kayayyaki. Ba su kadai ba ma, har da kasashe makwabta da nahiyar baki daya. Wannan lamari zai kara inganta kyautata rayuwar jama’a.

Na biyu, fiton kayayyaki. Wannan zai bunkasa karfin kasar na shiga kasuwannin duniya da ma kara haskata a dandalin kasa da kasa. Haka kuma zai kai ga bunkasa lamarin da zai bata karin damarmakin samun karin ci gaba ta fuskar kasuwanci da ababen more rayuwa tare da janyo jarin waje.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Na uku, samar da guraben ayyukan yi. Cikin watannin 9, wannan yankin masana’atu da Sin ta gina, ya samar da karin guraben ayyukan yi sama da 850 ga mazauna wurin. Daya daga cikin manyan abubuwan dake haifar da rashin ci gaba kasa da ma rikice-rikice shi ne yawaitar masu zaman kashe wando, amma da zarar aka samu ayyukan yi, to ya kan toshe kafofi da dama masu tarnaki ga ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al’umma.

A ganina, dangatakar Sin da kasar Habasha, ba samar da hanyar bunkasa tattalin arziki kadai ta yi ba, har ma da samarwa kasar irin dabarar kasar Sin ta samun ci gaba. Mun sani cewa, kasar Sin ta bullo da wata sabuwar hanyar ci gaba da ba a taba gani ba a duniya, inda take juya yawan al’umma da albarkatun da take da su a cikin gida zuwa hanyoyin bunaksa ci gabanta ba tare da mulkin mallaka ba. Hakika hulda da kasar Sin alheri ce, kuma na yi imanin sauran kasashen Afrika za su iya bin sawun Habasha don tabbatar da ci gabansu.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.