ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimakon Kasar Sin Na Ingiza Ci Gaba A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Kafofin yada labarai a kasar Habasha sun ruwaito a jiya cewa, yankin masana’antu na Kombolcha (KIP) da kasar Sin ta gina a kasar, ya samar da kimanin dala miliyan 28 na kudin shiga daga fiton kayayyaki zuwa ketare, cikin watannin 9 na farkon shekarar kudi ta kasar ta (2023/2024) da ta fara daga ranar 8 ga watan Yulin 2023.

Wannan ci gaba abun burgewa ne matuka, ganin yadda dukkan abubuwan da aka fitar, an samar da su ne a harabar yankin na KIP na kasar Habasha. Samar da yankin da kamfanin CCECC na kasar Sin ya gina, wani bangare ne na burin Habasha na zama cibiyar samar da kayayyaki a nahiyar Afrika, kuma da alama ta dauki hanyar cimma wannan buri nata, da taimakon kasar Sin.

  • Sin Ba Ta Da Masaniya Game Da Dalilin Philippines Na Kin Amincewa Da Daidaiton Da Aka Cimma Kan Batun Sashen Tudun Ruwa Na Ren’aijiao
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Sama Da 80% Sun Soki Yadda Japan Ta Gurbata Tarihi Cikin Sabbin Littattafan Da Ta Buga

Yayin da ake fama da hauhawar farashin kayayyaki da ma raguwar darajar kudaden kasashe musamman na Afrika, masana na cewa samar da kayayyaki a cikin gida, wata ingantacciyar dabara ce ta shawo kan matsaloli da dama. Tabbas Habasha ta samarwa kanta mafita, godiya ga kasar Sin. Zan bada misali da wasu batutuwa 3.

ADVERTISEMENT

Na farko, samar da kayayyaki a cikin gida. Yadda wannan yanki na KIP ke samar da kayayyaki a cikin gida, tabbas zai ragewa al’ummar kasar radadin hauhawar farashin kayayyaki. Ba su kadai ba ma, har da kasashe makwabta da nahiyar baki daya. Wannan lamari zai kara inganta kyautata rayuwar jama’a.

Na biyu, fiton kayayyaki. Wannan zai bunkasa karfin kasar na shiga kasuwannin duniya da ma kara haskata a dandalin kasa da kasa. Haka kuma zai kai ga bunkasa lamarin da zai bata karin damarmakin samun karin ci gaba ta fuskar kasuwanci da ababen more rayuwa tare da janyo jarin waje.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Na uku, samar da guraben ayyukan yi. Cikin watannin 9, wannan yankin masana’atu da Sin ta gina, ya samar da karin guraben ayyukan yi sama da 850 ga mazauna wurin. Daya daga cikin manyan abubuwan dake haifar da rashin ci gaba kasa da ma rikice-rikice shi ne yawaitar masu zaman kashe wando, amma da zarar aka samu ayyukan yi, to ya kan toshe kafofi da dama masu tarnaki ga ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al’umma.

A ganina, dangatakar Sin da kasar Habasha, ba samar da hanyar bunkasa tattalin arziki kadai ta yi ba, har ma da samarwa kasar irin dabarar kasar Sin ta samun ci gaba. Mun sani cewa, kasar Sin ta bullo da wata sabuwar hanyar ci gaba da ba a taba gani ba a duniya, inda take juya yawan al’umma da albarkatun da take da su a cikin gida zuwa hanyoyin bunaksa ci gabanta ba tare da mulkin mallaka ba. Hakika hulda da kasar Sin alheri ce, kuma na yi imanin sauran kasashen Afrika za su iya bin sawun Habasha don tabbatar da ci gabansu.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.