• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kaduna

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa shaidun babbar jam’iyyar adawa ta PDP da ke kalubalantar lashe zabensa ne suka tabbatar masa da nasara cikin rashin sani.

Ya bayyana hakan ne a jawabinsa na karshe ga kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kaduna, wanda tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Cif Bayo Ojo suka bayyana.

  • Hukuncin Kotun Zabe: Martanin Da Atiku Da Obi Suka Mayar Kan Tabbatar Da Nasarar Tinubu
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Babbar Jam’iyyar adawa ta kalubalanci ayyana Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar tare da dan takararta Mohammed Ashiru Isa, suna neman a sake sakamakon zabe.

A cikin karar da ake kalubalantar nasarar Uba Sani, masu shigar da kara sun kira shaidu 24 tare da gabatar da su a gaban kotu.

A ranar Litinin 4 ga watan Satumba, kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna ta kammala amsar dukkanin shaidun da aka gabatar mata, wanda a yanzu ana jiran yanke hukunci ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A cewar gwamnan, masu shigar da kara sun taimaka masa wajen tabbatar da nasararsa ta lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda suka yi nuni da karbi shaida daga, Bonett Gwazah, wani babban manazarcin sashen sadarwa a hukumar INEC na Jihar Kaduna.

Gwamnan ta bakin lauyansa ya ce, “Masu shigar da karar sun kira jimillar shaidu 24, wadanda akasarin bayanansu na rantsuwar an gabatar da su ne bisa sammacin da aka bayar a lokacin da ake sauraron karar.

“Bayan an rufe amsar shaidu, wanda ake kara bai da wata bukata ta kira shaidu, bayan da suka fitar da isassun shaidu a karkashin binciken da aka gudanar, wanda shaidun sun goyi bayan bangaren da ake kara”.

Kotun sauraron karar da ke karkashin mai ahari’a, Bictor Obiawie, ta yi alkawarin a kowane lokaci za ta yanke hukunc a nan gaba bisa adalci ga kowani bangare.

Ita ma hukumar zaben wadda ita ce farkon wacce aka shigar da koken a kanta, ta tabo batun wani kuskuren da masu shigar da kara suka yi kan amincewa da takardun zabe.

A halin da ake ciki kuma, dan takarar gwamnan Jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar PDP a zaben da ya gudana a ranar 18 ga Maris, 2023, Hon. Isa Ashiru, ya bayyana cewa sakamakon zabe guda biyu masu cin karo da juna da suka fito daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Jihar Kaduna, wanda a cewarsa, ya hana shi samun nasara a zaben.

Dan takarar gwamnan na PDP ya bayyana haka ne a gaban kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda ya kara jaddada cewa INEC ta sauya sakamakon zaben na asali domin bai wa jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Bayan gabatar da jawabinsa na karshe a rubuce a gaban alkalan kotun mai mutum 3 karkashin jagorancin Bictor Obiawie, Ashiru ta bakin babban lauyansa, Oluwole Iyamu ya bayyana cewa INEC ce ta sauya sakamakon zaben.

Ashiru ya kuma yi zargin cewa an samu kuri’u da suka wuce ka’ida da kuma kin bin tsarin zabe, yayin da ya yi kira da INEC kar ta bayyana sunan Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna.

A halin yanzu dai, bayan karbar hujjoji na karshe daga kowani bangare, kotun ta dage yanke hukunci har zuwa wata rana da za ta sanar da lauyoyin nan gaba.

A yanzu haka dai ana dakon yanke hukunci na karshe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Heilongjiang

Xi Ya Jaddada Bude Wani Sabon Babi Na Ci Gaban Heilongjiang Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.