• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talakawa Da Teloli Sun Bayyana Yadda Karamar Sallar Bana Ta Zo Musu

by Abubakar Abba
1 year ago
in Rahotonni
0
Talakawa Da Teloli Sun Bayyana Yadda Karamar Sallar Bana Ta Zo Musu

Saeed Muhammad

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka kammala Azumin watan Ramadan na banar, sun gudanar da shagulgulan bikin karamar Sallah, sai dai wasu sallah ta zo musu ba kamar yadda suka saba fantamawa a baya ba.

LEADERHIP Hausa ta jiyo ra’ayoyin wasu mazauna Jihar Kaduna, musamman talakawa da kuma teloli kan irin yanayin yadda karamar Sallar bana ta zo masu duba da matsin rayuwa.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
Talakawa
Aisha Usman

Wata mai suna Aisha Usman, wadda mijinta ya rasu ya bar mata marayu hudu ta ce, Sallar bana ba ta zo mata yadda ta yi tsammani ba, saboda matsin tattalin arziki da talauci. Ta ce da ba ta samu tallafin abincin daga wurin jama’a ba, da ba ta san yadda za ta ciyar da marayunta.

Ta ce maganar dinka masu kayan Sallah ma ba ta taso ba, ina kokarin samu abincin da za su ci gaba da ci bayan kammala Azumin.

Ibrahim Sani ya ce, duk da cewa ana cikin yanayin matsin rayauwa, wata uku kafin fara Azumin ya fara tanadin abincin da iyalisa za su yi amfani da shi da Azumin. A cewarsa, duk da matsin na tattalin arziki, hakan nan ya kukata ya samu ya yi wa iyalisa kayan Sallah, saboda al’adace da aka saba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Talakawa
Saeed Muhammad

  Shi kuwa Saeed Muhammad ya ce, karamar Sallar bana ta zo masa a cikin wani irin yanayin da bai taba samun kaisa a ciki ba, domin kuwa, ya saba a duk shekara yana tallafa wa iyayesa da abinci, musamman a watan Azumi baya ga iyalansa da suka zamo masa wajibi, sannn kuma ya yi masu dinke-dinken suturar Sallah.

Ya ce sai dai a bana, saboda irin halin kuncin rayuwa da al’ummar kasar nan suka tsinci kansu a ciki, abun sai dai kawai ya ce sun gode wa Allah tun da ya bar su da rai da lafiya har kuma sun samu damar azumtar watan Ramadan.

Talakawa
Mustapha Musa

Mustapha Musa ya ce, “Ni a yanzu ba na batun dinkin Sallah na yara, domin abun da ke gabana shi ne, in tanadar masu da abincin da za su ci a Sallar da kuma bayanta.”

A bangaren wasu teloli kuwa, akasarinsu sun ce bana ba harka domin Sallar ta zo masu a cikin bazata.

Talakawa
Ibrahim Adamu Tela

 Daya daga cikinsu, Adamu Ibrahim ya ce, “A bana ban samu yawan aikin dinkuna da na saba samu a baya ba, amma ina ganin matsin tattalin arziki da ya addabi jama’a ne, musamman talakawa, shi ya sa ban samu yawan tulin aikin dinki da na saba samu a shekarun baya ba, amma Alhamdulillahi ba laifi na samu aikin dinkuna wadanda za su toshe min wasu kafa na ciyar da iyalina.”

Shi kuwa Sani Kabiru ya danganta rashin samun masu kawo masa aikin dinkuna kan yadda wasu Musulman suka gwammace su siya wa ‘ya’yansu dinkakkun kayayyaki da ake sayarwa a kasuwa, wadanda ake yi wa lakabi da ‘Ishirun ka maraya’.Ya ce, hakan na da nasaba da yanayin matsin tattalin arziki da ake fuskanta a kasar.

Abudllahi Umar ya ce, “A Sallar bana, shagona ba masaka tsinke, saboda yawan aikin dinkunan da aka kawo min kusan wata biyu kafin fara Azumi, sai da na rufe karbar dinki saboda aikin da ke gabana ya yi min yawa. Sai duk da haka a bana ban samu rabin aikin da na ke samu ba.

 A ra’ayin Garba Awwal ya danganta rashin samun abokan hulda ne kan tashin gwaron farashin dala, wanda hakan ya janyo hauhawan farashin kayan masarufi, musaman kayayyakin abinci, hakan ya rage wa jama’a kawo aikin dinki.

 Ya ce yana gode wa Allah tun da an dan samu aikin da ba za a rasa ba, kuma yana ganin kila bayan Sallar idan an biya ma’aikata albashi za su kara samun aikin dinkin.

 Shi kuwa Mahadi Rabe ya ce, wasu telolin saboda irin kudin da suke tsawallawa na yin dikin ne ya sa ba su samun aikin dinki mai yawa a bana ba. A cewarsa, ba ya ganin laifin ‘yan’uwasa teloli ko da sun tsawalla farashi dinki domin kayan aiki sun tashi.

A nata ra’ayin, Aisha Abubakar ta danganta rashin aikin dinkin ne kan rashin samun wadatacciyar wutar lantarki, wanda don gudun kar telolin su ba su kunya saboda rashin wutar lantarkin.

 Ta kara dfa cewa saboda rashin wadatacciyar lantarkin dole ne sai sun sayi man fetur, wanda dole su kuma su kara cajin kudin aiki.

Ita ma Hau’uwa Yusuf ta bayyana cewa tana cikin hamdala, domin kuwa ba ta rasa samun aikin dinkin mata da yawa duk da yanayin halin kuncin da wasu jama’a suke a ciki.

Ta ce har rufe karbar dinki ta yi saboda ba ta so a bana ta janyo wa kaita zagi daga wurin masu kawo dinkin da ta iya kammala nasu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Na Hada Gidan Rediyon Da Ake Ji A Jihohi Takwas –Injiniya Yakubu

Next Post

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.