• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talakawa Da Teloli Sun Bayyana Yadda Karamar Sallar Bana Ta Zo Musu

by Abubakar Abba
1 year ago
in Rahotonni
0
Talakawa Da Teloli Sun Bayyana Yadda Karamar Sallar Bana Ta Zo Musu

Saeed Muhammad

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da al’ummar Musulmi a fadin duniya suka kammala Azumin watan Ramadan na banar, sun gudanar da shagulgulan bikin karamar Sallah, sai dai wasu sallah ta zo musu ba kamar yadda suka saba fantamawa a baya ba.

LEADERHIP Hausa ta jiyo ra’ayoyin wasu mazauna Jihar Kaduna, musamman talakawa da kuma teloli kan irin yanayin yadda karamar Sallar bana ta zo masu duba da matsin rayuwa.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine
Talakawa
Aisha Usman

Wata mai suna Aisha Usman, wadda mijinta ya rasu ya bar mata marayu hudu ta ce, Sallar bana ba ta zo mata yadda ta yi tsammani ba, saboda matsin tattalin arziki da talauci. Ta ce da ba ta samu tallafin abincin daga wurin jama’a ba, da ba ta san yadda za ta ciyar da marayunta.

Ta ce maganar dinka masu kayan Sallah ma ba ta taso ba, ina kokarin samu abincin da za su ci gaba da ci bayan kammala Azumin.

Ibrahim Sani ya ce, duk da cewa ana cikin yanayin matsin rayauwa, wata uku kafin fara Azumin ya fara tanadin abincin da iyalisa za su yi amfani da shi da Azumin. A cewarsa, duk da matsin na tattalin arziki, hakan nan ya kukata ya samu ya yi wa iyalisa kayan Sallah, saboda al’adace da aka saba.

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Talakawa
Saeed Muhammad

  Shi kuwa Saeed Muhammad ya ce, karamar Sallar bana ta zo masa a cikin wani irin yanayin da bai taba samun kaisa a ciki ba, domin kuwa, ya saba a duk shekara yana tallafa wa iyayesa da abinci, musamman a watan Azumi baya ga iyalansa da suka zamo masa wajibi, sannn kuma ya yi masu dinke-dinken suturar Sallah.

Ya ce sai dai a bana, saboda irin halin kuncin rayuwa da al’ummar kasar nan suka tsinci kansu a ciki, abun sai dai kawai ya ce sun gode wa Allah tun da ya bar su da rai da lafiya har kuma sun samu damar azumtar watan Ramadan.

Talakawa
Mustapha Musa

Mustapha Musa ya ce, “Ni a yanzu ba na batun dinkin Sallah na yara, domin abun da ke gabana shi ne, in tanadar masu da abincin da za su ci a Sallar da kuma bayanta.”

A bangaren wasu teloli kuwa, akasarinsu sun ce bana ba harka domin Sallar ta zo masu a cikin bazata.

Talakawa
Ibrahim Adamu Tela

 Daya daga cikinsu, Adamu Ibrahim ya ce, “A bana ban samu yawan aikin dinkuna da na saba samu a baya ba, amma ina ganin matsin tattalin arziki da ya addabi jama’a ne, musamman talakawa, shi ya sa ban samu yawan tulin aikin dinki da na saba samu a shekarun baya ba, amma Alhamdulillahi ba laifi na samu aikin dinkuna wadanda za su toshe min wasu kafa na ciyar da iyalina.”

Shi kuwa Sani Kabiru ya danganta rashin samun masu kawo masa aikin dinkuna kan yadda wasu Musulman suka gwammace su siya wa ‘ya’yansu dinkakkun kayayyaki da ake sayarwa a kasuwa, wadanda ake yi wa lakabi da ‘Ishirun ka maraya’.Ya ce, hakan na da nasaba da yanayin matsin tattalin arziki da ake fuskanta a kasar.

Abudllahi Umar ya ce, “A Sallar bana, shagona ba masaka tsinke, saboda yawan aikin dinkunan da aka kawo min kusan wata biyu kafin fara Azumi, sai da na rufe karbar dinki saboda aikin da ke gabana ya yi min yawa. Sai duk da haka a bana ban samu rabin aikin da na ke samu ba.

 A ra’ayin Garba Awwal ya danganta rashin samun abokan hulda ne kan tashin gwaron farashin dala, wanda hakan ya janyo hauhawan farashin kayan masarufi, musaman kayayyakin abinci, hakan ya rage wa jama’a kawo aikin dinki.

 Ya ce yana gode wa Allah tun da an dan samu aikin da ba za a rasa ba, kuma yana ganin kila bayan Sallar idan an biya ma’aikata albashi za su kara samun aikin dinkin.

 Shi kuwa Mahadi Rabe ya ce, wasu telolin saboda irin kudin da suke tsawallawa na yin dikin ne ya sa ba su samun aikin dinki mai yawa a bana ba. A cewarsa, ba ya ganin laifin ‘yan’uwasa teloli ko da sun tsawalla farashi dinki domin kayan aiki sun tashi.

A nata ra’ayin, Aisha Abubakar ta danganta rashin aikin dinkin ne kan rashin samun wadatacciyar wutar lantarki, wanda don gudun kar telolin su ba su kunya saboda rashin wutar lantarkin.

 Ta kara dfa cewa saboda rashin wadatacciyar lantarkin dole ne sai sun sayi man fetur, wanda dole su kuma su kara cajin kudin aiki.

Ita ma Hau’uwa Yusuf ta bayyana cewa tana cikin hamdala, domin kuwa ba ta rasa samun aikin dinkin mata da yawa duk da yanayin halin kuncin da wasu jama’a suke a ciki.

Ta ce har rufe karbar dinki ta yi saboda ba ta so a bana ta janyo wa kaita zagi daga wurin masu kawo dinkin da ta iya kammala nasu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Na Hada Gidan Rediyon Da Ake Ji A Jihohi Takwas –Injiniya Yakubu

Next Post

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

Related

Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

9 hours ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

1 week ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

1 week ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

1 week ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 weeks ago
Next Post
Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

LABARAI MASU NASABA

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.