ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (4)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
Manzon Allah

Alhamdu lillah. Masu karatu muna muku barka da Sallah. Muna kauna daga Allah, ya karbi ibadunmu, ya ba mu zaman lafiya da ci gaba a kasarmu da duk kasashen musulmi har ma da duniya baki daya.

Idan ba a manta ba, kafin watan Ramadan ya kama, darasinmu a wannan shafin yana bayani ne a kan rantsuwar da Allah ya yi da uba da dan da ya haifa wanda Malamai suka fassara mana cewa, uban ana nufin Annabi Ibrahim (AS) dan da uban ya haifa kuma ana nufin Annabi (SAW). Duka dai nuni ne a kan rantsuwa da darajar Manzon Allah (SAW).

  • Girman Darajar Manzon Allah S.A.W Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (3)
  • Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (2)

Za mu ci gaba kamar haka: A wani wuri kuma, a cikin Alkur’an maigirma inda Allah ta’ala ya ce “Alif lam miym, zalikal kitaab…”, Sayyidina Abdullahi bin Abbas (RA) ya ce wadannan haruffan rantse-rantse ne da Allah ya yi da su. Ma’ana Allah ya rantse da Alif, ya rantse da Lam kuma ya rantse da Minjaye. Allah ya rantse da su sai ya ce a (aya ta gaba) “wannan littafin (Alkur’ani) babu kokwanto a cikinsa”.

ADVERTISEMENT

Sahlu Abdullahis Tustari ya ce wannan rantsuwa ce, ma’anar Alif din nan tana nufin “farkon sunan Allah”, ita kuwa Lamin tana nufin “karshen sunan Mala’ika Jibrilu”, sannan Minjaye tana nufin “farkon sunan Muhammadu”. Malam Samarkandi ya ruwaito wannan fassarar. To, idan aka tafi a kan wannan fassarar ta Tustari da Samarkandi, ma’anar wannan rantsuwar daga Alifun ita ce wato kamar Allah ya ce ne “Ni ne Allah, na saukar da Jibrilu zuwa ga Muhammadu da wannan littafin da babu kokwanto a ciki”. Malamai sun ce ko a nan ya isa a ga girman Manzon Allah (SAW). Suka ce, Alif da aka rantse da shi farkon sunan Allah ne, Minjaye da aka rantse da ita farkon sunan Annabi ne ‘Muhammadu’ amma da yake ba a shiga tsakanin Allah da Manzon Allah’ sai shi Mala’ika Jibrilu aka dauko karshen sunansa, wato Lamin din nan. Da shi ma dauko farkon sunansa za a yi, abin sai ya zama Alif (na Allah), Jiymun (na Jibrilu) da Miymun (na Muhammadu SAW). Wannan ma manuniya ce a kan girman Manzon Allah a wurin Allah (SWT).

Sannan har ila yau, an sanya Jibrilu a tsakani ne don koya wa halitta baki daya yadda za su rika bin wasida ko tsani na neman abu. Misali, kar mutum ya ce zai nemi ilimi amma shi zai karantar da kansa da kansa, ba zai je wurin wani malami ba. Ko mutum zai yi sana’a amma ya ce da kansa zai yi ba tare da ya samu wani ubangida ya koya masa ba. Wannan fassarar Samarkandi ya ruwaito ta ce ta hanyarsa, bai ce daga Tustari ne ba. Wato kowa yana da hanyarsa daban.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

A wata fuskar kuma, wadannan haruffan Allah ya rantse da su ne cewa wannan littafin gaskiya ne babu kokwanto a cikinsa. Har ila yau, hada sunan Allah da na Manzon Allah a cikin haruffan yana nuna matsayi da girman Manzon Allah (SAW).

Malam Ibn Ada’u ya ce, ayar ‘Kaaf’ (Suratu Kaaf) rantsuwa ce da Allah ya yi da karfin zuciyar masoyinsa (SAW). Zuciyar Manzon Allah tana da karfi sosai fiye da yadda ake iya tunani. Domin Alkur’ani da Allah ya saukar a zuciyar Manzon Allah ya saukar kuma ta iya daukawa, da za a saukar wa dutse zai ragargaje. Amma kuma sai ga shi; shi (Manzon Allah) an saukar masa a zuciyarsa kuma ya iya daukawa.

Zuciyar Manzon Allah (SAW) ita ce babbar na’urar da ta iya daukar Alkur’ani saboda nauyinsa (kaulan thakiylan) har sauran al’umma suka samu sauki suna iya daukawa.

Haka nan, zuciyarsa (SAW) ta iya daukar ganin Allah. Shi Annabi Musa (AS) da aka yi masa tajalli sai da ya fadi ya suma. Amma Annabi (SAW) bai suma ba, ba ma kawai bai yi haka ba kadai; hatta al’ummarsa ma bai manta da su ba. Gafara da rahamar da ya roka wa al’ummarsa (a cikin Bakara) duk a gaban Zatin Allah aka yi su. Wannan ya isa ya nuna karfin Annabi. Shi Annabi Musa (AS) ma Malamai sun ce Zatin Allah da ya yi Tajalli ko girman kan allura bai gani ba.

Watakila kuma aka ce wannan harafi na “Kaaf”, sunan Kur’ani ne, ma’ana Kur’anu, wannan Kahuwau din farkon sunan Kur’ani ne, to kuma Allah ya yi rantsuwa da Kur’ani ne a gaba kuma ya kara kawo rantsuwar da sunan Kur’ani kuru-kuru? To, Malamai dai sun fadi haka. Watakila kuma aka ce “Kaaf” sunan Allah ne. Kila kuma “Kaaf” wani dutse ne da ya kewaya duniya ana ce ma sa “Jabalu Kaaf”. Akwai duntsen da ya kewaya duniya, sannan kuma duwatsun kankara suka kewaya. Wannan dutsen da shi Allah ya yi wa duniya Katanga don kar ta kife ko ta yi yawo da mu. Su kuma duwatsun kankara Allah ya kewaya duniya da su don kar rana ta kona mu. Haka kuma an ce fassarar “Kaaf” wanin wannan ne.

Sayyidina Ja’afara bin Muhammadus Sadik (Sharifi dan Manzon Allah SAW) ya ce, ana fassara rantse-rantsen da Allah ya yi a Alkur’ani da Manzon Allah ne. In ma dai Allah ya rantse da Zuciyar Manzon Allah ko kuma da Manzon Allah dukansa (SAW). Sayyidina Ja’afarus Sadik ya fassara rantsuwar da Allah ya yi da “Wannajmi” a matsayin Manzon Allah. Ma’anar “Wannajmi” a zahiri, Allah ya yi rantsuwa ne da Tauraron Surayya idan ya fadi. Amma a wurin Ja’afarus Sadik, ana nufin Annabi Muhammadu ne (SAW). Ya ce, wannan tauraron Zuciyar Annabi Muhammadu ne. Zuciyar Manzon Allah abu ne mai girma, sirri ne mai girma a wannan wurin. Don haka ya ce rantsuwar da Allah ya yi da “Wannajmi”, ya yi ne da Manzon Allah. Fassarar “izhaa hawaa” kuma ba yana nufin idan tauraro ya fadi ba ne, yana nufin yalwar Zuciyar Manzon Allah ne. Ya kuma ce, a wata fassarar, Allah ya rantse da zuciyar Manzon Allah ne don ta yanke ga barin komai sai Allah. Manzon Allah babu kowa a gabansa sai Zatin Allah. A koyaushe yana cikin Zikirin Allah. Makka gari ne na Aljannu, in kana duba tarihin Makka za ka ga haka. A nan ne Jinnun Nasibiyn suka zo suka ba da gaskiya da shi. Wurin da kowa yake tsoron zuwa amma shi Manzon Allah haka zai rika shiga cikin dare, cikin duwatsu da kogo yana ta Zikiransa. Da akwai tsoron wani ba Allah ba, zai iya firgita shi.

Alkur’ani ya zo da rantse-rantse da yawa. Akwai rantsuwa ta harafi, kamar “Alif-lam-miym”, akwai rantsuwa ta kalma, kamar ya ce “Wannajmi izhaa hawaa” ko ya ce “Wasshamsi wa duhaahaa”. Wadannan rantse-rantse ilimi ne mai yawa. Kuma an ce asirai ne na Allah Tabaraka wa Ta’ala.

Shehu Ibrahim Inyass (RTA) a cikin Tafsirinsa na ayar “Kaaf…”, yake cewa akwai halaye guda uku da muke da su. Akwai halin zuciya na Dan Adam, akwai halin aiki na Dan Adam, akwai halin harshe na Dan Adam. Haka Musulunci ma yake, Musulunci kudircewa ne a zuciya, fada ne da baki, aiki ne da jiki. Ka kudirce babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, ka fadi La’ilaha illallah da baki, sannan a ga kana aiki da jiki wurin yin Sallah da Azumi da sauransu. To, a duk cikin wadannan halayen guda uku, akwai wani hali da ba mu san shi ba sai dai bin Allah kawai. Misali, a cikin halin aiki, ba mu san mece ce ma’anar mu je mu debi duwatsu muna jifa da su a wani waje da sunan muna jifan shaidan ba. Domin mu ba shaidan din muka gani ba, ba shaidan din kuru-kuru a wajen amma kuma tun da Shari’a ta yarda a yi, Manzon Allah (SAW) ya fada mana shikenan sai aikatawa kawai. Ko mun iya ganewa, ko ba mu iya ganewa ba dole mu yi. Haka idan aka dubi ibadar Safa da Marwa, tafiya ake yi a tsakanin wani dutse zuwa wani, amma tun da Shari’a ce ta ce a yi, sai a yi kawai ko mun gane; ko ba mu gane ba. Haka nan Arfa, zama za mu yi a wurin, an yarda mu yi Sallar Azuhur da La’asar a nan, amma ba a yarda mu yi Magriba da Isha’i a nan ba don ma kar mu zaci Sallah ta zaunar da mu a nan sai mun kai Muzdalifa. A can kuma zama kawai ake so mu yi. Ka ga duk wadannan sai dai bi kawai, babu tilas sai mun gane kafin mu yi. Ma’anar irin wadannan ibadun ba kowane Musulmi ne ya sani ba, amma kuma suna kan kowane Musulmi ya aikata da ya samu damar zuwa Hajji. Tun da Allah ne ya ce a yi shikenan sai aikatawa kawai, walau ka gane ko ba ka gane ba. Wannan hali na aikinmu kenan.

Haka nan a cikin kudircewarmu, Manzon Allah ya ba mu labari cewa mu yi imani da Allah kuma sako ne daga Allah. Mun yi imani ba tare da cewa dole sai mun ga Allah ba.

Manzon Allah
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 3, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Next Post
Bobrisky

Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗaure Bobrisky Wata 6 Ba Tare Da Zaɓin Biyan Tara Ba

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.