• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ne ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin duniya na kin mafarkin murdiya. Tarihi ya nuna mana cewa, tabbatar da adalci ya kasance alkiblar al’ummar dan Adam ta dindindin. Ko da yake a wani lokaci mugunta ta samu damar mai da hannun agogo baya, amma a karshe abubuwa za su koma daidai.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, lokacin da motocin yaki na Jamus suka murkushe kauyuka a kasashen gabashin Turai, kuma jiragen saman yaki na Japan suka jefa bama-bamai a kasar Sin da mai da biranenta zuwa kufai: da alama kasashen sun kasance masu karfi da ba za su taba shan kaye ba. Amma a karkashin turjiyar mutane masu adalci na duniya, ‘yan mulkin zalunci ba za su iya magance faduwar totuwa da fuskantar hukunci a karshe ba. Mugunta ba za ta iya lashe adalci ba, wannan yana cikin ka’idojin tarihi.

  • Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
  • Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Sai dai har yanzu, bil’adama suna ci gaba da fuskantar ayyukan dake neman mai da hannun agogo baya: tunanin mulkin danniya, da ra’ayi na daukar matakin kashin kai, da na kariyar ciniki, suna yaduwa a duniya. Wasu kasashe sun kaddamar da yakin cinikayya da na haraji, wadanda suka yi matukar illata tattalin arzikin duniya da kuma karya dokokin cinikayya na kasa da kasa. Amma masu kare adalci suna nan a ko da yaushe, wadanda ke kokarin mayar da duniya kan turba mai dacewa, kuma kasar Sin na daya daga cikinsu.

A gun taron kolin BRICS da aka gudanar jiya ta yanar gizo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda uku a cikin jawabinsa: Wato tsayawa kan manufar cudanyar sassa daban-daban, da kiyaye daidaito da adalci a duniya; da tabbatar da bude kofa da cin moriya tare, don kare tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa; da kuma tabbatar da hadin kai a kokarin samun ci gaba na bai daya. Wadannan shawarwari, sun kunshi kalmomi na nuna sassaucin ra’ayi, amma ma’anarsu na cike da adalci. Suna wakiltar martanin kasar Sin game da yunkurin mayar da hannun agogo baya da ake fuskanta a halin yanzu a fagen kasa da kasa, wadanda ke nuna yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da gaskiya da adalci, da neman hadin kai, da sa kaimi ga tabbatar da moriyar juna a duk fadin duniya. Wannan tsari na adalci shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin samun cikakken goyon baya daga mafi yawan kasashen duniya.

Tabbas, ya kamata a kiyaye adalci ta hanyar aikace-aikace maimakon magana. Mu dauki yakin haraji da Amurka ta kaddamar kan Afirka a misali: Bayan da Amurka ta sauya manufarta ta ciniki da kasashen Afirka, da sanya musu harajin fito mai yawa da ya kai kaso 15 zuwa kaso 30 cikin 100, nan da nan kasar Sin ta fara taimakawa kasashen Afirka, inda ta sanar da cewa, za ta yafe dukkan harajin da ake karba kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla hulda da ita, suka fitar zuwa cikin gidanta. Wannan matakin ya aike da wani sako mai kyau ga Afirka, wato kasar Sin na son raba damar samun ci gaba tare da kasashen Afirka, da hadin kai da su don tinkarar hadurra. Lamarin da ya samu yabo daga masana tattalin arziki na kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kana wasu alkaluman da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta fitar sun nuna cewa, a cikin watanni 7 na farkon wannan shekara, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashe mafi karancin ci gaba a nahiyar Afirka, wadanda Sin ta riga ta yafe musu dukkan haraji, ta kai dalar Amurka biliyan 39.66, adadin da ya karu da kaso 10.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin a bara. Ta hanyar karfafa hadin gwiwar cinikayya da abokan hulda kamar Sin, da inganta cinikayya a cikin nahiya, ana sa ran ganin Afirka za ta samu nasarar rage tasirin manufar harajin Amurka.

A halin yanzu, kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin da kasashen Afirka, suna kokarin daukaka ra’ayin cudanyar sassa daban daban, da na bude kofa, da yin hadin gwiwa tare da tabbatar da moriyar juna, da hadin kai da juna, a karkashin laimar tsare-tsaren hadin gwiwa irin na BRICS, kuma suna tafiya zuwa gaba kan wata turba mai adalci. Tabbas babu wani karfi da zai iya hana su cimma buri da samun nasara. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Next Post

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

4 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

4 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

5 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

6 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

7 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

1 week ago
Next Post
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.