• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gandun Dajin Yankari Da Halin Da Yake Ciki

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Yankari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarar 1934 kwamitin gwamnatin Arewacin Nijeriya ya ba da shawara ga kwamitin zartarwa cewa a kirkiro wurin bude ido da shakatawa da wucin gadi a masarautar Bauchi. Alhaji Muhammadu Ngeleruma, shi ne Ministan aikin gona da albarkatun kasa karkashin tsohuwar gwamnatin Arewa ya ji dadin wata tafiyar da ya yi zuwa filin shakatawa da bude ido na kasar Sudan lokacin da ya je aiki a Afirka ta gabas.

Lokacin da ya dawo sai ya ba da shawarar a bude irin shi a Nijeriya.
A shekarar 1956 gwamnatin Jihar Arewa ta amince da shirin da aka yin a samar da wurin da za a kafa wurin shakatawa da bude idanu. Sai aka amincewa da sunan Yankari a matsayin wurin da yafi dacewa a Kudu a wancan lokacin ana kiran wurin Lardin Bauchi inda akwai manyan namun daji da yawa wadanda wurin suke zama za kuma a kare su. A shekarar 1957 ne aka ware wurin inda aka sa ma shi suna a karkashin hukumar kulawa da gandun daji ta Bauchi.

  • An Gano Ciwon Ciki Da Ke Turnuke Sojojin Isra’ila A Gaza
  • Kungiya Ta Yi Kira Da A Gaggauta Bincike Kan Harin Soji A Kauyen Tudun Biri 

An bude Yankari a karo na farko ga mutane a matsayin wurin shakatawa na Firimiya ranar 1 ga Disamba 1962. Tun wancan lokacin ne gwamnatin Arewacin gabashin da jihar Bauchi tare suka fara kulawa da wurin.
Wurin shakatawa ko bude ido naYankari wani babban wurin yawo bude ido ne ko shakatawa da ya taba kasancewa a karkashi gwamnatin tarayya a kudu maso tsakiyar Jihar Bauchi a sashen Arewa maso gabas na Nijeriya.

Wuri ne mai tsawon murabba’in kilomita 2,244 km2 (866 sk mi),bugu da kari wurine na abubuwa masu burgewa da ban sha’awa.Yana a cikn yanayin da zai burge da kayata mutane saboda kasancewar inda yake yammacin Afirka inda yake da dabbobi wadanda wurin ka same su.Wurin shakatawa ko bude ido na Yankari an kirkiro shi ne a shekarar 1956 tun kafin a samu mulkin kai, amma daga baya an mai da shi babban wurin shakatawa na kasa a shekarar 1991.Wurin shakatawa ne wanda ya yi suna wajen baki da su zo yawan bude ido a Nijeriya, ya bada muhimmiyar gudunmawa wajen bunkasa harkar shakatawa da abubuwa masu daukar hankali da aka same su a wurin.

Wurin shakatawa na Yankari kauyuka sun zagaye shi da suke da manoma da makiyaya, sai dai kuma ba wani abin da ya nuna dan Adam ya taba zama a wurin fiye da shekaru dari da suka wuce. Sai dai kuma akwai alamun da suke nuna mutane sun taba zama a wurin da suka hada da,tsofaffin karafa da wani wurin da ake samar da wuta ta yin aiki, duk da yake a karshen shekarar 1990 akwai irin abubuwan fiye da hamsin a Delimiri da Ampara.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiYankari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Ni Da Burin Da Ya Wuce Na Samu Kuɗi A Kannywood – Garzali Miko

Next Post

Yadda Ake Amfani Da Ruwan Shinkafa Wajen Gyaran Jiki

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

1 month ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

2 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

7 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

10 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

11 months ago
Yankari
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

12 months ago
Next Post
Ruwan Shinkafa

Yadda Ake Amfani Da Ruwan Shinkafa Wajen Gyaran Jiki

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.