• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Masarautu
0
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gusau ita da wasu wuraren da suke makwabtaka da ita an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa sun kasance ne a cikin birnin na masarautar.A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambo da hedikwatarta take a Gusau tana da wasu garuruwa da suke har ila yau karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da Gusau, kamar sauran sassan na daular Usumaniyya.

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki bayan da akwai wadanda suke taimakawa ita Gusau din wajen tafiyar mulki, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa shi garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayen su suke  haka,Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Sune suke wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni,da kuma Sarkin katsinan Gusau (Emir Of Gusau).Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarki.Gusau kamar sauran sassan da suke karkashi daular Usumaniyya suna aikawa da kason fadar Sarkin musulmi na irin kudaden da ta samu.

  • Rikicin Masarautar Kano: Tinubu Da Sanusi II Suna Da Alaka Mai Karfi – Fadar Shugaban Kasa
  • Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’oin cigaba na garin Gusau da kungiyoyin da suke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa ma kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna, da wasu harkoki, manyan kamfanoni duk an kawo ma shi birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasa ta cigaban zamani.

Sai dai duk da haka wasu tsare- tsaren mulkin mallaka da aka kawo sune suka sauya salo na mulkin.Idan ba haka b agarin na Gusau bai kai a rika  ba shi girma da daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanen lokaci lamurra sai suka canza.Lokacin mulkn mallaka na turawa ne aka fa amsar harajin dabbobi a shekarar 1907 da ake kira da suna  (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne sana’ar noma ta kasance babbar abar da take bunkasa tattalin arziki na garin Gusau,abin kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma.Sana’ar noma ta zama ba tad ana biyu idan ana maganar tattalin arziki ne wadda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona a ci da kuma sayarwa

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806- 1827

Wadannan Sarakunan shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida1916-1917

Sai dai kuma daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan da ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba Sarkin Katsinan Gusau 1984- 2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GusauMasarautaPalace
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Next Post

Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara – Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

Related

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

8 months ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

1 year ago
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

1 year ago
Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
Masarautu

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

1 year ago
Tinubu Zai Halarci  Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa
Addini

Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

1 year ago
A Tsarin Mulki, Sarkin Musulmi Ba Shi Da Ikon Naɗa Wani – Gwamnatin Sokoto
Manyan Labarai

A Tsarin Mulki, Sarkin Musulmi Ba Shi Da Ikon Naɗa Wani – Gwamnatin Sokoto

1 year ago
Next Post
Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara – Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara - Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.