ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Gusau

Gusau ita da wasu wuraren da suke makwabtaka da ita an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa sun kasance ne a cikin birnin na masarautar.A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambo da hedikwatarta take a Gusau tana da wasu garuruwa da suke har ila yau karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da Gusau, kamar sauran sassan na daular Usumaniyya.

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki bayan da akwai wadanda suke taimakawa ita Gusau din wajen tafiyar mulki, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa shi garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayen su suke  haka,Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Sune suke wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni,da kuma Sarkin katsinan Gusau (Emir Of Gusau).Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarki.Gusau kamar sauran sassan da suke karkashi daular Usumaniyya suna aikawa da kason fadar Sarkin musulmi na irin kudaden da ta samu.

  • Rikicin Masarautar Kano: Tinubu Da Sanusi II Suna Da Alaka Mai Karfi – Fadar Shugaban Kasa
  • Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’oin cigaba na garin Gusau da kungiyoyin da suke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa ma kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna, da wasu harkoki, manyan kamfanoni duk an kawo ma shi birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasa ta cigaban zamani.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da haka wasu tsare- tsaren mulkin mallaka da aka kawo sune suka sauya salo na mulkin.Idan ba haka b agarin na Gusau bai kai a rika  ba shi girma da daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanen lokaci lamurra sai suka canza.Lokacin mulkn mallaka na turawa ne aka fa amsar harajin dabbobi a shekarar 1907 da ake kira da suna  (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne sana’ar noma ta kasance babbar abar da take bunkasa tattalin arziki na garin Gusau,abin kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma.Sana’ar noma ta zama ba tad ana biyu idan ana maganar tattalin arziki ne wadda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona a ci da kuma sayarwa

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806- 1827

Wadannan Sarakunan shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida1916-1917

Sai dai kuma daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan da ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba Sarkin Katsinan Gusau 1984- 2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

January 12, 2025
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

July 31, 2024
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

July 22, 2024
Next Post
Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara – Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

Ku Daina Alaƙanta Ni Da Ƴan Bindigar Zamfara - Matawalle Ya Gargadi Yan Adawa

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.