• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (4)

Ci gaba daga makon daya gabata

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (4)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A lokacin da Sarkin Zazzau Malam Muhammadu Makau ya fita ya zuwa Sallar Idi. Su Wadancan masu bore sun rufe kofar Gari suka hana shi komawa cikinta.

A dalilin haka Sarki Muhammadu Makau sai bai wani ja da su ba, domin a tunaninsa jama’arsa ne kuma bai da bukatar yakar kasarsa, amma sai ya juya akalar dokinsa ya nausa cikin kasashen Nufawa da sauran kabilu don bude wata daula daban.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Kwastam Reshen Tashar Jiragen Ruwan Apapa Ta Tara Naira Biliyan 489 Cikin Wata Uku

Kafin  ya bar kasar Zazzau ya yi dakata a bayan gari inda ya tattara jama’arsa.

Wancan wuri a yau shi ake kira da  suna Dakace (Dakacen Sarki).Ya cimma nasarar yin hakan wajen kafa wuri (wuraren da a yau suka zama masarautu biyu wadanda ake kiransu da sunayen kannensa a halin yanzu wato Sule-ja (Sulaimanu- sza) da Abu-ja (Abubakar- sza).

Wancan wurin ne a yau ya zama zuciyar kasar baki daya.Tarihi ya nuna cewar daga baya ya yi yunkurin fadada sabuwar daularsa ta wajen yakar ko kwatar wasu bangarori na kasar Zazzau duk da a lokacin tsufa ya kama shi sai ya umurci danuwasa Sulaimanu Ja da ya koma ya rike sabuwar daularsa gudun kar ta kubuce masu baki daya; inda ya sa shi a matsayin wakilinsa.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

Bayan rasuwar Sarki Muhammadu Makau sai Malam Sulaimanu ya zama sabon sarki.

Wannan wuri daga baya an raba shi biyu inda su wadancan kanne na Sarkin Zazzau Muhammadu Makau suka mai da su wuraren masarautunsu kuma aka sanya wa wuraren sunayensu.

Dalilin raba wa ‘yan-uwasa wannan wuri zai ta’allaka a kan samar da zaman lafiya a zuriyarsu kuma su shugabanci wadannan sabbin dauloli don kauda tunaninsu ga komawa cikin birnin Zazzau.

Wannan ba karamin tunani ne ba, ga shugabanni adalai masanan ya kamata da hangen nesa.

Daga wa]annan wurare basu sake tunanin kafa wata daula ko fadada kasa ba.Sai dai tarihin baya na shi Sarki Muhammadu inda ya yi yunkurin kwato wasu yankuna da ke karkashin kasar Zazzau ya zuwa sabuwar masarautarsa kuma wannan yunkuri ya cimma ajalinsa.

Shehu ]an Fodio ya yi fama da jama’arsa ko ince mabiyansa a }arken jihadinsa.Domin sun juya al’amarin ya zuwa neman mulki ba wai kokarin da’awa da jaddada addinin Allah; da daukaka addinin Allah ba.

Almajiran Shehu sun mai da hankali wajen neman mulkan jama’a ko ta halin ya ya.

Manufar Shehu shi ne na kauce wa shirka da kadaita Allah (S.W.A) abin bauta shi kadai kuma su maida duk al’amurransu ga Allah shi kadai.

Amma‘yan shirkokin da ba a rasa su ba tun daga mabiyansa har ya zuwa ga sauran jama’a. Allah (subhanahu wata’ala) ya sa ya cimma nasara ta dagewa a kan akidarsa ba tare da jin tsoro ko shakkun wani abin da zai same shi ba.

Duk wadancan nasarori sun samu ne ta wajen dagewar da Shehu tare da kaninsa Abdullahi da kuma dansa Muhammad Bello, su ka yi bisa yardar Allah.

Mahara daga cikin daliban Shehu Mujaddadi,wadanda son mulki ta yaudara, sun tafi ya zuwa kasashen Borno da Yobe da Taraba da kuma Bauchi, inda suka tarad da Malam Rabeh Fadel Allah ya yi nisa da shigowa wajan jihadinsa.Wannan za a iya gani tun daga cikin kasar Nijer har ya zuwa kasashen da na yi bayani a baya.

Kamar yadda tarihi ya nuna mana cewar kafin karshen jihadin da gudana a zamanin Shehu Usmanu, dalibansa sun yi yunkurin kai jihadinsa kasashen gabashin kasashen Arewa wanda bai samu dama ba don tuni addini Musulunci ya yi karfi sai dai fadan siyasa kawai.

A littafi mai sun “ Language Disappearance, case study of Biu Emirate” na Bukar Usman ya yi kokarin bayanin yadda ta kwashe tsakanin Mujaddadi Rabeh Fadel Allah tare da dansa Fadarallah da masarautun wadannan kasashe a tsakanin shekara ta 1755zuwa 1809.

Rabe ya nausa kasar Borno dansa kuma ya nausa }asar Biu har ya zuwa Wuyo wanda ake kira da suna Bayo a halin yanzu cikin kasar Borno.

Wannan ya faru ne a tsakanin shekarar 1893 zuwa 1901. A dalilin wannan tashin-tashina na jahadin wanda wadancan Shehunnai biyu suka yi, ya kawo kai-komon jama’a daga wannan waje zuwa wancan waje,musamman ga jama’ar Biu a wancan karni.

Hujjojin wannan bayani an samo su ne ta wajan zantawa da jama’a daban daban, wanda ya nuna cewar jama’a sun taru daga Arewacin masanin ba a gabashin Nijer da Borno zuwa kudancin wannan kasa. Misali jama’ar Biu sun nuna cewar akwai wurare biyu wanda yake duk asalin wurin mazaunansu ne (wurin zamansu),kamar Yemen da Chadi.

Majiya:- Hausa Wikepedia


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa

Next Post

Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

1 month ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

2 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

7 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

10 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

11 months ago
Zazzau
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

12 months ago
Next Post
Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.