ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

by CGTN Hausa
2 years ago
default

default

A ‘yan kwanakin nan, wasu kasashen yammacin duniya sun sha zargin kasar Sin da “samar da hajoji fiye da kima”, wadanda a cewarsu, wai kayayyakin da masana’antun kasar Sin suka samar, musamman ma motocin lantarki, da batirin Lithium, da farantan samar da lantarki ta hasken rana, wadanda “suke cika kasuwannin duniya cikin farashi mai matukar rahusa”, kuma “Yadda kasar Sin ke samar da hajoji fiye da kima ka iya haifar da barazana ga bunkasuwar masana’antun sauran kasashe, har da tattalin arzikin duniya.” 

Amma a hakika, a zargin da suke yi wa kasar Sin, Amurka da kungiyar tarayyar Turai sun bayyana “samar da hajoji fiye da kima” a matsayin yadda ake samar da hajoji fiye da bukatun gida, wanda bai dace ba. Idan mun yi nazari, kaso 1/5 na amfanin gonar da manoman kasar Amurka suke samarwa ana fitar da su ne ga kasar Sin, kuma daga cikin motoci kimanin miliyan 4.1 da kamfanonin samar da motoci na kasar Jamus suka kera a bara, miliyan 3.1 ne aka fitar da su zuwa kasashen ketare. To, idan “samar da hajoji fiye da kima” na nufin yadda ake samar da hajoji fiye da bukatun gida, ko wadannan kasashe ma suna samar da hajojinsu fiye da kima? Idan kuma hakan ne, yaya za a yi da ciniki a tsakanin kasa da kasa?

  • Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa
  • Falasdinawa Na Komawa Khan Younis Yayin Da Isra’ila Ta Janye Dakarunta

Ban da haka, bisa lissafin da hukumar kula da makamashi ta duniya ta yi, an ce, ya zuwa shekarar 2030, adadin motoci masu aiki da sabbin makamashi da ake bukata a fadin duniya zai kai miliyan 45, wanda ya ninka na shekarar 2022 har sau 4.5. Sa’an nan, yawan wutar lantarki da aka samar ta hasken rana da ake bukata za ta ninka na shekarar 2022 har sau 4. Ta hakan muna iya gano cewa, akwai babban gibi a tsakanin kayayyakin da ake samarwa da ma bukatun kasuwanni, musamman bukatar kasashe masu tasowa ta fannin kayayyaki masu aiki da sabbin makamashi. Abin da mutanen kasashen yamma suka fada na wai “kasar Sin na samar da kayayyaki fiye da kima”, sam ba gaskiya ba ne.

ADVERTISEMENT

Motocin lantarki, da batirin Lithium, da farantan samar da lantarki ta hasken rana da kasar Sin ke samarwa, suna samun matukar karbuwa a kasuwannin duniya ne sabo da yadda kamfanonin kasar Sin suka dukufa a kan kirkire-kirkiren fasahohi, da kasuwar kasar mai matukar girma, da cikakken tsarin masana’antun kasar, da ma daidaiton da kasa da kasa suka cimma na tinkarar sauyin yanayi. Har ila yau, kayayyaki masu inganci na kasar Sin na biyan bukatun kasashen duniya, a sa’in da kasar ke ba da gudummawarta a kokarin da kasa da kasa ke yi na tinkarar sauyin yanayi.

A lokacin da ake kokarin tinkarar sauyin yanayin duniya, wasu mutanen kasashen yamma suna alakanta matsalar da ake fuskanta da karancin sabbin makamashin da aka samar, amma su ne suke zargin kasar Sin da samar da sabbin makamashi “fiye da kima”. Ta bangaren shige da fice na motoci kuma, yawan motocin lantarki da kasar Sin ta fitar zuwa Turai ya kai kaso 8% ne kawai na kasuwannin kasashen Turai, amma an ce kasar ta samar da motoci fiye da kima, a yayin da aka daukaka kasar Jamus a matsayin kasa mai karfi wajen samar da motoci, bisa yadda take fitar da kusan kaso 80% na motocin da ta samar zuwa ketare. Kasashen yamma suna zancen ‘yancin ciniki a lokacin da kayayyakinsu ke da fifiko, amma sun zargi kasar Sin da haifar da barazana ga kasuwannin duniya sabo da yadda kayayyakin da ta samar ke samun karbuwa.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Lallai, bunkasuwar kasar Sin ce take haifar wa wasu kasashen yamma rashin jin dadi. Saurin bunkasuwar masana’antun samar da sabbin makamashi na kasar Sin na sa su damuwa, don haka ma suke shafa wa kasar Sin bakin fenti don neman dakile bunkasuwarta, tare da kiyaye babakeren da suka kafa a tsarin masana’antun samar da kayayyaki na duniya. Kasashen yamma sun yi ta fakewa da furucin nan na wai “kasar Sin na haifar da barazana”, don samar da dalili na yin kariyar ciniki.

Kasar Sin tana da ‘yancin tabbatar da bunkasuwarta, al’ummar Sinawa ma suna da ‘yancin tabbatar da rayuwa mai walwala. A yayin da suke kokarin cimma wannan buri, kasar Sin ta bunkasa da kara karfinta, amma ba don neman zarce wasu, ko haifar da barazana ga wasu, ko kuma maye gurbin wasu ba. A maimakon haka, tana son raba nasarorin da ta cimma tare da kasashen duniya, sabo da a ganinta, jirgi daya ne kasashen duniya suke ciki, kuma dole ne su hada kawunansu don tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya.

Duk wanda ke neman shatile wasu, hakan ba zai kara masa saurin tafiya ba. (Lubabatu Lei)

 

Shatile
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Yadda Aiki A Kamfanin Gine-gine Ya Jefa Rayuwar Matashi Cikin Hatsari

Yadda Aiki A Kamfanin Gine-gine Ya Jefa Rayuwar Matashi Cikin Hatsari

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.