ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (4)

Ci gaba daga makon daya gabata

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zazzau

A lokacin da Sarkin Zazzau Malam Muhammadu Makau ya fita ya zuwa Sallar Idi. Su Wadancan masu bore sun rufe kofar Gari suka hana shi komawa cikinta.

A dalilin haka Sarki Muhammadu Makau sai bai wani ja da su ba, domin a tunaninsa jama’arsa ne kuma bai da bukatar yakar kasarsa, amma sai ya juya akalar dokinsa ya nausa cikin kasashen Nufawa da sauran kabilu don bude wata daula daban.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Kwastam Reshen Tashar Jiragen Ruwan Apapa Ta Tara Naira Biliyan 489 Cikin Wata Uku

Kafin  ya bar kasar Zazzau ya yi dakata a bayan gari inda ya tattara jama’arsa.

ADVERTISEMENT

Wancan wuri a yau shi ake kira da  suna Dakace (Dakacen Sarki).Ya cimma nasarar yin hakan wajen kafa wuri (wuraren da a yau suka zama masarautu biyu wadanda ake kiransu da sunayen kannensa a halin yanzu wato Sule-ja (Sulaimanu- sza) da Abu-ja (Abubakar- sza).

Wancan wurin ne a yau ya zama zuciyar kasar baki daya.Tarihi ya nuna cewar daga baya ya yi yunkurin fadada sabuwar daularsa ta wajen yakar ko kwatar wasu bangarori na kasar Zazzau duk da a lokacin tsufa ya kama shi sai ya umurci danuwasa Sulaimanu Ja da ya koma ya rike sabuwar daularsa gudun kar ta kubuce masu baki daya; inda ya sa shi a matsayin wakilinsa.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Bayan rasuwar Sarki Muhammadu Makau sai Malam Sulaimanu ya zama sabon sarki.

Wannan wuri daga baya an raba shi biyu inda su wadancan kanne na Sarkin Zazzau Muhammadu Makau suka mai da su wuraren masarautunsu kuma aka sanya wa wuraren sunayensu.

Dalilin raba wa ‘yan-uwasa wannan wuri zai ta’allaka a kan samar da zaman lafiya a zuriyarsu kuma su shugabanci wadannan sabbin dauloli don kauda tunaninsu ga komawa cikin birnin Zazzau.

Wannan ba karamin tunani ne ba, ga shugabanni adalai masanan ya kamata da hangen nesa.

Daga wa]annan wurare basu sake tunanin kafa wata daula ko fadada kasa ba.Sai dai tarihin baya na shi Sarki Muhammadu inda ya yi yunkurin kwato wasu yankuna da ke karkashin kasar Zazzau ya zuwa sabuwar masarautarsa kuma wannan yunkuri ya cimma ajalinsa.

Shehu ]an Fodio ya yi fama da jama’arsa ko ince mabiyansa a }arken jihadinsa.Domin sun juya al’amarin ya zuwa neman mulki ba wai kokarin da’awa da jaddada addinin Allah; da daukaka addinin Allah ba.

Almajiran Shehu sun mai da hankali wajen neman mulkan jama’a ko ta halin ya ya.

Manufar Shehu shi ne na kauce wa shirka da kadaita Allah (S.W.A) abin bauta shi kadai kuma su maida duk al’amurransu ga Allah shi kadai.

Amma‘yan shirkokin da ba a rasa su ba tun daga mabiyansa har ya zuwa ga sauran jama’a. Allah (subhanahu wata’ala) ya sa ya cimma nasara ta dagewa a kan akidarsa ba tare da jin tsoro ko shakkun wani abin da zai same shi ba.

Duk wadancan nasarori sun samu ne ta wajen dagewar da Shehu tare da kaninsa Abdullahi da kuma dansa Muhammad Bello, su ka yi bisa yardar Allah.

Mahara daga cikin daliban Shehu Mujaddadi,wadanda son mulki ta yaudara, sun tafi ya zuwa kasashen Borno da Yobe da Taraba da kuma Bauchi, inda suka tarad da Malam Rabeh Fadel Allah ya yi nisa da shigowa wajan jihadinsa.Wannan za a iya gani tun daga cikin kasar Nijer har ya zuwa kasashen da na yi bayani a baya.

Kamar yadda tarihi ya nuna mana cewar kafin karshen jihadin da gudana a zamanin Shehu Usmanu, dalibansa sun yi yunkurin kai jihadinsa kasashen gabashin kasashen Arewa wanda bai samu dama ba don tuni addini Musulunci ya yi karfi sai dai fadan siyasa kawai.

A littafi mai sun “ Language Disappearance, case study of Biu Emirate” na Bukar Usman ya yi kokarin bayanin yadda ta kwashe tsakanin Mujaddadi Rabeh Fadel Allah tare da dansa Fadarallah da masarautun wadannan kasashe a tsakanin shekara ta 1755zuwa 1809.

Rabe ya nausa kasar Borno dansa kuma ya nausa }asar Biu har ya zuwa Wuyo wanda ake kira da suna Bayo a halin yanzu cikin kasar Borno.

Wannan ya faru ne a tsakanin shekarar 1893 zuwa 1901. A dalilin wannan tashin-tashina na jahadin wanda wadancan Shehunnai biyu suka yi, ya kawo kai-komon jama’a daga wannan waje zuwa wancan waje,musamman ga jama’ar Biu a wancan karni.

Hujjojin wannan bayani an samo su ne ta wajan zantawa da jama’a daban daban, wanda ya nuna cewar jama’a sun taru daga Arewacin masanin ba a gabashin Nijer da Borno zuwa kudancin wannan kasa. Misali jama’ar Biu sun nuna cewar akwai wurare biyu wanda yake duk asalin wurin mazaunansu ne (wurin zamansu),kamar Yemen da Chadi.

Majiya:- Hausa Wikepedia

Zazzau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

Shatile Wasu Ba Ya Karawa Mai Yin Hakan Saurin Tafiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.