• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mu’ammar Muhammad Abu Minyar Gaddafi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Tarihin Mu’ammar Muhammad Abu Minyar Gaddafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shi dai Muammar Gaddafi, shi ne tsohon shugaban kasar Libya, ya rayu daga shekara ta 1942 zuwa 20 ga watan Oktoba shekara ta 2011), Muammar al-Gaddafi da larabci:
Am fi saninsa da Kanal Gaddafi ko Gaddafi, ya kasance dan gwagwarmayar kasar Libya ne, Dan siyasa, kuma mai taimakon mutanensa.

Ya mulki kasar Libiya matsayinsa na jagoran juyin mulkin da ta samar da Jamhuriyyar Larabawa ta Libya wato Libyan Arab Republic da turanci, tun daga shekara ta 1969 har zuwa 1977, sannan aka canja sunan jagorancinsa zuwa Shugaba Dan’uwa wato “Brotherly Leader” na babbar jam’iyar talakawa, da akafi sani da Great Socialist People’s Libyan Arab Jamahiriya tun daga shekara ta 1977 har zuwa shekaran 2011.

  • Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

Gaddafi ya kasance dan rajin ci gaban Larabawa ne amma daga baya ana ganin ya watsar da hakan ya fara bin ra’ayin kansa.
Gaddafi ya rike mukamai da dama a ciki da wajen kasarsa, daga ciki ya rike shugaban kungiyar kasashen Afirika wato African Union (AU) daga 2 ga Fabrairun shekarar 2009 har zuwa 31 ga watan Janairu. Gaddafi ya yi karatunsa a Jami’ar Kasar Libya da kuma Jami’ar Soji ta Benghazi, Gaddafi Musulmi ne, mai bin ahlus-Sunnah, wato sunni Islam.

Tarihinsa.
An haifI Gaddafi a kusa da garin Sirte daga gidan talakawa makiyayan Larabawa, Gaddafi mai matukar kishin Larabawa ne tun yana makaranta a Sabha, daga nan ya shiga Royal Military Academy, Benghazi.
Yana cikin soja ne ya hada kungiyar da ta kifar da mulkin Turawan Yamma a kasar wanda suke amfani da sarkin kasar na wancan lokacin wato Senussi Mulkin Idris a shekarar 1969.

Daga amsar mulki, Gaddafi ya sauya Libiya daga mulkin sarauta zuwa jamhuriyya inda ‘yan gwagwarmayarsa ke mulki da umurninsa.

Labarai Masu Nasaba

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Daga nan ne ya kora dukkani Italiyawa da Turawan dake da sansani a kasar zuwa kasashensu, kuma ya karfafa dangantakarsa da sauran kasashen Larabawa, musamman da Shugaba Gamal Abdel Nasser’s na kasar Misra (Egypt) tare da neman hadin kan kasashen Afirika.

Gaddafi ya kafa Shari’a a matsayin abin gudanar da dokokin kasar, tare da daukar tsarin jagoranci Musulunci.

Ya mayar da arzikin man fetur din kasar mallakar gwamnati kuma ya rika amfani da kudaden domin karfafa sojojin kasar, da taimaka wa kasashen waje, da taimaka wa mutane wurin ginin gidaje, kiwon lafiya, ilimi da sauransu.

Gaddafi ya sauya fasalin Kasar Libya zuwa mulkin da ya kira “Jamahuriyya” wato kasar al’ummah da Turanci (“state of the masses”) a shekarar 1977.

A shekara ta 1970s zuwa 1980s, yakin iyaka tsakanin Libya da kasashen Misra da Cadi da taimakon ‘yan tawayen kasashen waje, da zargin da ake masa na daukar nauyin Lockerbie bombing a kasar Scotland ya sa kasar ta zama saniyar ware a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Amfani Da Batun Sinadarin Fentanyl Wajen Kakaba Takunkumai Ga Bangaren Sin

Next Post

Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

Related

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

1 hour ago
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

3 hours ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

4 hours ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

5 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

5 hours ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

8 hours ago
Next Post
Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.