• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mu’ammar Muhammad Abu Minyar Gaddafi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Tarihin Mu’ammar Muhammad Abu Minyar Gaddafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shi dai Muammar Gaddafi, shi ne tsohon shugaban kasar Libya, ya rayu daga shekara ta 1942 zuwa 20 ga watan Oktoba shekara ta 2011), Muammar al-Gaddafi da larabci:
Am fi saninsa da Kanal Gaddafi ko Gaddafi, ya kasance dan gwagwarmayar kasar Libya ne, Dan siyasa, kuma mai taimakon mutanensa.

Ya mulki kasar Libiya matsayinsa na jagoran juyin mulkin da ta samar da Jamhuriyyar Larabawa ta Libya wato Libyan Arab Republic da turanci, tun daga shekara ta 1969 har zuwa 1977, sannan aka canja sunan jagorancinsa zuwa Shugaba Dan’uwa wato “Brotherly Leader” na babbar jam’iyar talakawa, da akafi sani da Great Socialist People’s Libyan Arab Jamahiriya tun daga shekara ta 1977 har zuwa shekaran 2011.

  • Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

Gaddafi ya kasance dan rajin ci gaban Larabawa ne amma daga baya ana ganin ya watsar da hakan ya fara bin ra’ayin kansa.
Gaddafi ya rike mukamai da dama a ciki da wajen kasarsa, daga ciki ya rike shugaban kungiyar kasashen Afirika wato African Union (AU) daga 2 ga Fabrairun shekarar 2009 har zuwa 31 ga watan Janairu. Gaddafi ya yi karatunsa a Jami’ar Kasar Libya da kuma Jami’ar Soji ta Benghazi, Gaddafi Musulmi ne, mai bin ahlus-Sunnah, wato sunni Islam.

Tarihinsa.
An haifI Gaddafi a kusa da garin Sirte daga gidan talakawa makiyayan Larabawa, Gaddafi mai matukar kishin Larabawa ne tun yana makaranta a Sabha, daga nan ya shiga Royal Military Academy, Benghazi.
Yana cikin soja ne ya hada kungiyar da ta kifar da mulkin Turawan Yamma a kasar wanda suke amfani da sarkin kasar na wancan lokacin wato Senussi Mulkin Idris a shekarar 1969.

Daga amsar mulki, Gaddafi ya sauya Libiya daga mulkin sarauta zuwa jamhuriyya inda ‘yan gwagwarmayarsa ke mulki da umurninsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Daga nan ne ya kora dukkani Italiyawa da Turawan dake da sansani a kasar zuwa kasashensu, kuma ya karfafa dangantakarsa da sauran kasashen Larabawa, musamman da Shugaba Gamal Abdel Nasser’s na kasar Misra (Egypt) tare da neman hadin kan kasashen Afirika.

Gaddafi ya kafa Shari’a a matsayin abin gudanar da dokokin kasar, tare da daukar tsarin jagoranci Musulunci.

Ya mayar da arzikin man fetur din kasar mallakar gwamnati kuma ya rika amfani da kudaden domin karfafa sojojin kasar, da taimaka wa kasashen waje, da taimaka wa mutane wurin ginin gidaje, kiwon lafiya, ilimi da sauransu.

Gaddafi ya sauya fasalin Kasar Libya zuwa mulkin da ya kira “Jamahuriyya” wato kasar al’ummah da Turanci (“state of the masses”) a shekarar 1977.

A shekara ta 1970s zuwa 1980s, yakin iyaka tsakanin Libya da kasashen Misra da Cadi da taimakon ‘yan tawayen kasashen waje, da zargin da ake masa na daukar nauyin Lockerbie bombing a kasar Scotland ya sa kasar ta zama saniyar ware a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Amfani Da Batun Sinadarin Fentanyl Wajen Kakaba Takunkumai Ga Bangaren Sin

Next Post

Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

4 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

5 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

6 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

7 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

9 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

11 hours ago
Next Post
Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.