ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Omar el-Bashir

An haifi shugaban kasar ta Sudan Omar al-Hassan Ahmad Bashir a shekara ta 1945 a garin Hoshe Bannaga mai tazarar kilomita 100 daga yankin Arewa maso Gabashin birnin Khartoum.

Ya kuma fara karatunsa na babar makarantar Middile ta Ahlia dake garin Shendi, daga nan ne kuma mahaifansa suka yi kaura zuwa birnin Khartoum a can din kuma ya kammala iliminsa na sakandre.

  • Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki

Shugaban kasar dai ta Sudan ya ci gaba da daukar nauyin karatunsa ne da irin taimakon da yake samu na kudade daga mahaifansa da kuma dan abin da yake samu a lokacin da ya yi aiki a wani garejin gayaran motoci a birnin na Khartoum.

ADVERTISEMENT

Bayan da shugaban kasar ta Sudan Omar al-Bashir ya kammala iliminsa na sakandre, ya shiga makarantar horar da sojin sama ta kasar Sudan, inda har ya sami horo na tuka jirgin sama.

A nan din ne kuma sami baban mukami a tskanin dakarun saman kasar Sudan, kafin kuma daga bisani ya zama shugaban Brigade din sojojin kasa na kasar Sudan.
Tsohon shugaban Kasar Sudan Omar Hassan Ahmad al-Bashir, ya sami manyan degrori biyu na Masters a fanin kimiyyar ayyukan soji, a kwalegen horars da kwamandojin soji ta Sudan da kuma kasar Malaysiya.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Haka zalika al-Bashir ya halarci kwalejin horas da soji ta birnin Cairo,inda har ya shiga cikin sojin kasar Masar, a lokacin da masar din ta yi yaki da Isra’ila a shekara ta 1973.
A shekara ta 1988, an nada Omar al-Bashir kan mukamin kwamandan Birgde ta 8 ta sojin Sudan a yankin Kudancin Sudan, inda aka dora masa alhakin yaki da yan tawayen Kudancin Sudan.

A watan Yuni na 1988 shida wasu manyan hafsoshin soji, sun hambarar da zababbiyar gwamnatin hadin kan kasa, karkashin shugabancin Sadik Al-Mahdi.

Manufofin gwamnatin Al-Bashir game da dabaka tsarin shariar musulunci a Sudan, ta haifar masa da rashin fahimtar juna tsakaninsa da alumomin Kudancin Sudan da mafi yawansu suka kasance Kiristoci, wanan dalili ne ma ya kara rura wutar fadan yan tawayen Kudancin Sudan.

A lokacin da Janar al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan ta hanyar juyin mulki irin na soji a ranar 30 ga watan Yunin 1989, an rika tabbatar da cewa anya al-Bashir zai iya rike ragamar mulkin kasar ta Sudan da yakin basasa ya daidaita.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan yana da shekaru 42 a duniya, kuma shi ne din ke zaman jami’in soji na farko da suka taka muhimiyar rawa wajen kai farmaki kan alumomin Kudancin Sudan.
Kasar dai ta Sudan an kasa ta kashi biyu, tsakanin Larabawa Musulmi na Arewaci da kuma kiristoci dake zaune a Kudancin na Sudan.

Kungiyar ‘yan tawayen Sudan ta SPLA ta fara yakin neman ‘yanci ne a shekara ta 1983, kuma tun daga wanan lokacin ne, kafin ma mulkin al-Bashir gwamnatocin da suka gabata, sun yi yaki da ‘yan tawayen Kudancin Sudan.

Kungiyar Afuwa ta Duniya ta kiyasta cewa, kimanin al’ummar kasar ta Sudan miliyan daya suka rasa rayukan su, sakamakon yakin basasar da ya barke a kasar, yayin kuma al’ummar ta Sudan miliyan 4.5 suka yi gudun hijira, zuwa wasu kasahe na ketare don tsira da rayukansu.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulki daga Sadek al-Mahdi a shekara ta 1989, da sunan ceto kasar Sudan daga hali na kaka na ka yi da ta sami kanta a ciki, ya sami goyon bayan Hassan al-Turabi shugaban jama’iyar National Islamic Front, kafin kuma daga karshe suka raba gari da juna, a lokacin da al-bashir ya rushe majalisar dokokin Sudan, ya kuma dauki matakai na soke dukanin jama’iyun siyasa dama kafofin yada labarun Sudan.

Omar el-Bashir
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Matawalle Ya Gwangwaje Jama’ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

Matawalle Ya Gwangwaje Jama'ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.