ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mu’ammar Muhammad Abu Minyar Gaddafi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Gaddafi

Shi dai Muammar Gaddafi, shi ne tsohon shugaban kasar Libya, ya rayu daga shekara ta 1942 zuwa 20 ga watan Oktoba shekara ta 2011), Muammar al-Gaddafi da larabci:
Am fi saninsa da Kanal Gaddafi ko Gaddafi, ya kasance dan gwagwarmayar kasar Libya ne, Dan siyasa, kuma mai taimakon mutanensa.

Ya mulki kasar Libiya matsayinsa na jagoran juyin mulkin da ta samar da Jamhuriyyar Larabawa ta Libya wato Libyan Arab Republic da turanci, tun daga shekara ta 1969 har zuwa 1977, sannan aka canja sunan jagorancinsa zuwa Shugaba Dan’uwa wato “Brotherly Leader” na babbar jam’iyar talakawa, da akafi sani da Great Socialist People’s Libyan Arab Jamahiriya tun daga shekara ta 1977 har zuwa shekaran 2011.

  • Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

Gaddafi ya kasance dan rajin ci gaban Larabawa ne amma daga baya ana ganin ya watsar da hakan ya fara bin ra’ayin kansa.
Gaddafi ya rike mukamai da dama a ciki da wajen kasarsa, daga ciki ya rike shugaban kungiyar kasashen Afirika wato African Union (AU) daga 2 ga Fabrairun shekarar 2009 har zuwa 31 ga watan Janairu. Gaddafi ya yi karatunsa a Jami’ar Kasar Libya da kuma Jami’ar Soji ta Benghazi, Gaddafi Musulmi ne, mai bin ahlus-Sunnah, wato sunni Islam.

ADVERTISEMENT

Tarihinsa.
An haifI Gaddafi a kusa da garin Sirte daga gidan talakawa makiyayan Larabawa, Gaddafi mai matukar kishin Larabawa ne tun yana makaranta a Sabha, daga nan ya shiga Royal Military Academy, Benghazi.
Yana cikin soja ne ya hada kungiyar da ta kifar da mulkin Turawan Yamma a kasar wanda suke amfani da sarkin kasar na wancan lokacin wato Senussi Mulkin Idris a shekarar 1969.

Daga amsar mulki, Gaddafi ya sauya Libiya daga mulkin sarauta zuwa jamhuriyya inda ‘yan gwagwarmayarsa ke mulki da umurninsa.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Daga nan ne ya kora dukkani Italiyawa da Turawan dake da sansani a kasar zuwa kasashensu, kuma ya karfafa dangantakarsa da sauran kasashen Larabawa, musamman da Shugaba Gamal Abdel Nasser’s na kasar Misra (Egypt) tare da neman hadin kan kasashen Afirika.

Gaddafi ya kafa Shari’a a matsayin abin gudanar da dokokin kasar, tare da daukar tsarin jagoranci Musulunci.

Ya mayar da arzikin man fetur din kasar mallakar gwamnati kuma ya rika amfani da kudaden domin karfafa sojojin kasar, da taimaka wa kasashen waje, da taimaka wa mutane wurin ginin gidaje, kiwon lafiya, ilimi da sauransu.

Gaddafi ya sauya fasalin Kasar Libya zuwa mulkin da ya kira “Jamahuriyya” wato kasar al’ummah da Turanci (“state of the masses”) a shekarar 1977.

A shekara ta 1970s zuwa 1980s, yakin iyaka tsakanin Libya da kasashen Misra da Cadi da taimakon ‘yan tawayen kasashen waje, da zargin da ake masa na daukar nauyin Lockerbie bombing a kasar Scotland ya sa kasar ta zama saniyar ware a duniya.

Gaddafi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

Wasu Masanan Afirka Na Sa Ganin An Dakatar Da Gudanar Da Cinikayya Da Kudin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.